Goron sallah 8 daga (kitabu was-sunnah) ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Sunday 9 July 2017

Goron sallah 8 daga (kitabu was-sunnah)

*GORON SALLAH-8???!!!*
.
.
*DAGA ZAUREN*
.
*KITABU WAS SUNNAH*
.
.
*ﻣﺠﻠﺲ ﺘﻌﻠﻴﻢ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ*
📓📔
Watsaps
08036222795
08136182627
:
Yau 14-10-1438, wacce tayi dai dai da 8-7-2017***
:
Taken Lekca
.
*GORON SALLAH-8*
-
Wannan shine bayani na Takwas
....
....
*ﺇﻥ ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ، ﻧﺤﻤﺪﻩ ﻭﻧﺴﺘﻌﻴﻨﻪ، ﻭﻧﺴﺘﻐﻔﺮﻩ، ﻭﻧﻌﻮﺫ ﺑﺎﻟﻠﻪ ﻣﻦ ﺷﺮﻭﺭ ﺃﻧﻔﺴﻨﺎ، ﻭﺳﻴﺌﺎﺕ ﺃﻋﻤﺎﻟﻨﺎ، ﻣﻦ ﻳﻬﺪﻩ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻼ ﻣﻀﻞ ﻟﻪ، ﻭﻣﻦ ﻳﻀﻠﻞ ﻓﻼ ﻫﺎﺩﻱ ﻟﻪ، ﻭﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺣﺪﻩ ﻻ ﺷﺮﻳﻚ ﻟﻪ ﻭﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻣﺤﻤﺪﺍ ﻋﺒﺪﻩ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ*
.
_Bayan haka Idan ba,a mantaba bayanin baya mun tuqe ne akan hadisin musulintar Abu zarri wanda yake cikin sahihu muslim kamar yadda nafada to yanzu kuwa akanshine zamu dora*****_
              _Bayan Annabi (s.a.w) yagama dawafi yazo yayi sallah sesuka koma gefe guda can suka zauna Shida Sayyidina Abubakar, ganin haka sai Abu zarri yazo yasamu Annabi Muhammad (s.a.w) sai yace masa Assalamu'alaika ya Rasulullah****_
                _Wannan itace Ranar farko wacce aka fara Furta wannan kalma ga Annabi Muhammad (s.a.w) wato Abu Zarri shine kenan Mutum na farko wanda yafara yiwa Annabi (S.a.w) sallama, kafinshi babu wanda yata6a yiwa Annabi gaisuwa ta hanyar sallama irin wannan****_
                _Se manzon Allah (s.a.w) ya amsa masa da Wa'alaika warahmatullah*****_
          _Se Annabi yace masa waye kai?? seyace ni daga qabilar Ghifar nake***_
        _Se Annabi yace masa, Tun yaushe kake anan garin?? Yace: Nakasance awannan wajen tsawon kwanaki 30 dare da yini, Sai Annabi yasake tambayarsa to waye yake ciyar dakai har kwanaki 30 dare sa yini??? Seyace: Banida wani abinci face wannan ruwan na Zam Zam******_
               _To kunjifa jama'a kwanaki 30 Abu zarri bayacin Komai baya shan komai face wannan ruwa na Zam zam wanda shikuma Abu Zarri a wannan lokacin bafa musulmi bane be riga ya musulintaba****_
              _Abu Zarri yacigaba da cewa kaga Wannan ruwan kawai nakeshafa ya manzon Allah amma kaga nayi qiba ya Manzon Alllah banajin wani alamar yunwa acikn zuciyata gashi nayi te6a cikina har yayi tattara***_
           _Se manzon Allah yace aidama shi yanada Albarka sannan kuma abincine ga me jin yunwa yana qosarwa*****_
           _Kunga wannan hadisin Na Abuzzari yana nuna mana cewa Ruwan Zam zam kanshi abincine wanda zaka iya riqonsa kullun ka dinga sha batareda kaji yunwa kokuma ka buqaci wani abinci dan yunwa ba sedai kaci saboda sha'awa****_
_Wannan Hadisin Na Abu Zarri ku ajje manashi, acan gaba zamuzo muku da ambaton yadda aka samu wasu jama'a suka riqe wannan ruwa na Zam zam matsayin abinci na wani lokaci me tsawo*****_
               _Imamul Baihaqi acikin littafinsa yakawo wani Hadisinda yake cewa Annabi (s.a.w) yakasance yanasawa ayi guzirin Zam zam acikin salka idan za,a fita fagen yaqi ana cika salkuna da tuluna, idan aka samu wayanda akaji musu raunika afagen dagar se azoda Ruwan Zam Zam adinga yayyafa musu****_
            _Wannan ruwaya ta Imamul Baihaqi tana nuna mana cewa Ashe ruwan Zam zam maganine ga wanda yaji ciwo, dan haka ko yanzu idan mutum yaji rauni walau hatsari yayi kodai wani sababi yasameshi yaji raunin to idan akwai Zam Zam akusa dashi to yasamu ya wanke wannan ciwon dashi, da ikon Allah ciwon zeyi saurin warkewa*****_
             _Ga kuma wannan Hadisin wanda Ibnu Majah ya ruwaito:_
*ﻗَﺎﻝَ : ﺮ َﺳُﻮﻝ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺻَﻠَّﻰ ﺍﻟﻠﻪُ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﻭَﺳَﻠَّﻢَ ﻳَﻘُﻮﻝُ : ﻣَﺎﺀُ ﺯَﻣْﺰَﻡَ، ﻟِﻤَﺎ ﺷُﺮِﺏَ ﻟَﻪُ*
*MANZON ALLAH (S.A.W) YACE: RUWAN ZAM ZAM YANA MATSAYIN DUK ABINDA AKASHA DOMINSA******
           _Kenan wannan hadisin yana nuna mana cewa duk abinda yasaka kasha ruwan zam zam sabodashi to zaka samu biyan buqatarka*****_
            _Wannan hadisin malamai sunkai ruwa rana sosai akanshi kamar yadda Sweedy ya ambata wayansu malamai sukace ya Inganta, wayansu kuma sukace bai ingantaba, Amma Nasirudden Albani kanshi ya inganta wannan hadisin acikin Sahihu Ibnu Majahi******_
            _Nan gaba kadan Insha Allahu zamu kawo muku yadda manyan malamai sukayi aiki da wannan hadisin alokacinda suke shan ruwan zam zam kuma zakuji irin yadda suka suka samu natija da biyan buqata*****_
:
:
Zamu dakata anan sekuma bayani nagaba Idan Allah yakaimu
=
=
_Almajirinku dan mutanen kabo_
'
_Jameel Alhassan Haruna Kabo_
_Alwahhaby-Assalafy_
.
 Nake mana fatan Alheri wassalamu alaikum
..
.
.
Zaku iya samun shafinmu na facebook tawannan hanyar
http://m.facebook.com/Kitabu-Wassunah-1522000298067561/
.
ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.

Subhanak Allahumma wabi hamdika ash hadu anla ila ha illah anta astagfiruka  Wa,atubu ilaika
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support