Duniya makaranta (fitowa ta 31) dr.mansur ibrahim sokoto ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Monday 31 July 2017

Duniya makaranta (fitowa ta 31) dr.mansur ibrahim sokoto

DUNIYA MAKARANTA

Fitowa ta 31

156. Idan ka kyautata ma mutum za ka mallake shi. Idan ka wadatu daga mutum za ka zama tsaran sa. Idan kuwa ka bukatu zuwa ga mutum, to dole sai ka zamo bawansa.

157. Tuntuben harshe ya fi tuntuben kafa zafi. Na kafa saurin warkewa yake yi, na harshe kuwa illanta mutum yake yi har karshen rayuwarsa.

158. Ilimi ya fi kudi, kuma ya fi mulki. Kai, har lafiya ma ya fi ta. Kudi da mulki da lafiya duk suna gushewa. Amma Ilimi yana nan tare da mai shi ba su rabuwa.

158. Abin al'ajabi da lura: Masallatai suna cika ne bayan isowar liman, amma filayen kwallo suna cika tun kafin zuwan 'yan wasa.

160. Kada lamarin duniya ya dame ka. Duk abin da ke cikin ta na Allah ne. Kada sha'anin arziki ya dame ka. Domin daga wurin Allah yake fitowa. Kada ka samu damuwa a kan gobe, domin a hannun Allah take. Abin da ya kamata ya dame ka shi ne, neman ka samu yardar Allah.


Rubutawa: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

6/11/1438
30/7/2017

» Gabatarwa Zauren Minbarin Malamai +2347037477743
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support