Masu hikima sunce ?? (fitowa ta 28) dr.mansur ibrahim sokoto ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Thursday 27 July 2017

Masu hikima sunce ?? (fitowa ta 28) dr.mansur ibrahim sokoto

MASU HIKIMA SUN CE

Fitowa ta 28

126. Idan ba ka son ka yi wa mutane aikin kirki, to, kayi musu yadda suka yi maka.

127. Idan makwaucinka ya ki ka, to, ka juyar da kofar gidanka. Sai ka huta, ya huta.

128. Amfanin hasken fitila na wadansu ne, ba nata ita kanta ba.

129. Kada karbar da mutane suke yi ma shawararka ya hana ka karbar tasu idan sun fada maka. Kada ka umurci mutane da alheri sannan ka kaurace masa.

130. Sau da yawa kakkan ki wani abu, amma ya same ka. Samuwarsa kuwa ta zama alheri ce gare ka. Sau da yawa kakan so samuwar wani abu, amma ka rasa shi. Kuma rashin nasa ya zama shi ne alheri gare ka.

Littafin: Sheikh Baba Ahmad As-Shinkidi

Fitarwa da gyarawa: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

2/11/1438
26/7/2017

» Gabatarwa Zauren Minbarin Malamai +2347037477743
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support