Duniya makaranta !! ( fitowa ta 25) dr.mansur ibrahim sokoto ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 25 July 2017

Duniya makaranta !! ( fitowa ta 25) dr.mansur ibrahim sokoto

DUNIYA MAKARANTA

Fitowa ta 25

121. Marar gaskiya kamar mai yagaggen wando ne, duk inda zai zauna sai ya rinka kame-kame. Mai gaskiya a natse yake zamansa.

122. An gane mimini ne a wurare guda uku: Idan ya samu ya gode ma Allah, idan ya rasa ya koka ma Allah, idan ya shiga damuwa ya koma ma Allah.

123. Abubuwa uku idan suka hadu da wasu uku ba su da magani: Talauci idan ya hafu da kasala. Kiyayya idan ta hadu da hassada. Jahilci idan ya hadu da girman kai. Allah ka sa mu gama da duniya lafiya.

124. Abubuwa uku ba su da tsada: Ilimi da Lafiya da Sadaki.

125. Idan kudi suka fara zance dole ne gaskiya ta rufe bakinta.

Rubutawa: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

29/10/1438
23/7/2017

» Gabatarwa Zauren Minbarin Malamai +2347037477743
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support