Duniyar aljannu da abinda ta kunsa ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Friday 7 July 2017

Duniyar aljannu da abinda ta kunsa

DUNIYAR ALJANU DA ABINDA TA KUNSA (01)
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM
**************************************
DON ALLAH IDAN KANA DA SAURIN TSORATA/FIRGITA, KAR KA KARANTA..
Mun gabatar da karatun ne a ZAUREN FIQHU WHATSAPP (3). Kuma ga yadda karatun ya kasance:
Duniyar Aljanu wata irin duniya ce wacce ta bambanta sosai da tamu duniyar. Ta wajen Kamanninta, da yanayinta, da kuma abubuwan da ta Qunsa.
Allah ya halicci Aljanu bisa siffofi nau'i uku kamar yadda Manzon Allah (saww) ya fada acikin wani hadisi.
Acikinsu akwai wadanda suke da Jikinsu shigen irin namu. Sai dai bambancin yanayin Qirar jikin da kuma girman halittar.
Akwai kuma wadanda Allah ya haliccesu ne abisa siffar Karnuka da Macizai. (Wadannan sune wadanda idan suna jikin mutum zai rika yawan mafarkin Karnuka ko Macizai, ko Qadangaru, etc).
Akwai kuma wadanda su acikin dazuzzuka suke yin rayuwarsu. Sai dai basu zama waje guda. Suna yawan tashi ne daga wani wajwn zuwa wani.
Duk wadannan abubuwan da nake fada, sun samo asali ne daga Alqur'ani da Hadisan Manzon Allah (saww) kuma Sahihan labarurruka sun tabbatar da haka.
Acikin nau'i na farko akwai masu yanayin Qirar jikin 'Dan Adam, suna da kai, suna da jiki da Qafafu da hanaye. Sai dai sun bambanta da na Bil Adama.
Misali akwai masu ido 'daya RAK atsakiyar goshinsu. Akwai kuma wadanda idanunsu ya tsage ne daga sama zuwa Qasa. Akwai masu bindi (jela) da komai irin na halittar Birrai (Monkey).
Wani kuma bakinsa ya fara ne tun daga jikin Kunnensa zuwa daya Kunnen. Wani kuma Hakora ne dashi kamar irin na Damisa ko Zaki. Wani kuma bakinsa kamar irin na Kada ne ( Crocodile).
Wasu kuma suna da yanayin halitta irin na Halittun cikin ruwa. Wasu kuma kamar halittun kan tudu suke.
Wato suna da Kofato, Fukafukai, Qaho, da sauransu. (sune wadanda idan sun shiga jikin 'Dan Adam zai rika yawan mafarkin Shanu suna binsa aguje, ko kuma mafarkin faduwa daga tsauni mai nisa).
Allah ya huwace musu su rika chanza launi, ko Siffar jikinsu zuwa ga wata halittar daban.
Shi yasa akan samu wadanda suke rikida su shigo cikin 'yan Adam har arika yin harkokin kasuwanci ko wata hulda dasu ba tare da an ganesu ba.
Musamman alokacin aikin Hajji, da yawa daga cikinsu sukan zo su chudanya da Bil Adama domin gudanar da ibadarsu. (wadannan muminai ne basa chutar da Bil Adama).
Akwai wanda ya ta'ba gaya mun cewa yayi shekaru fiye da hamsin yana harkokin kasuwancinsa anan cikin Birnin Kano. Yana chinikayya da mutane amma babu wanda yasan cewa shi Aljani ne. (wani dan uwansa ne ya shiga jikin wata Baiwar Allah, shine nace masa yazo ya zama shaida akan dan uwan nasa).
Duk wanda ya taba zama acikin tsangayun Karatun Alqur'ani, zai samu labarin wasu irin aljanu Musulmai Muminai. Ana kiransu da suna "TSOMA".
Suna shigowa tsangayu har ana yin karatun Alqur'ani tare dasu. Kuma wani lokacin suna taimakon Mutane da addu'a ko lakanin samun karatu (Wannan ya faru sosai).
Akwai kuma Qananan yaransu sukan zo suyi wasa acikin yaran Bil Adama. Ba tare da wani babba ya ganesu ba.
Akwai kuma wawayen cikinsu wadanda sukan shigo duniyar Bil Adama domin gudanar da ayyukan sabon Allah. Kamar Zina, Sata, Tsafi, harka da bokaye, etc.
Babban abinda ke tsaremu daga sharrin Miyagun cikinsu shine Alqur'ani da Zikirin Allah. Don haka sai mu rike sosai.
Anan zamu tsaya sai wani lokacin kuma zamu sake lekawa cikin duniyar tasu, bisa hasken Alqur'ani da Sunnar Manzon Rahama (saww).
DAGA ZAUREN FIQHU WHATSAPP 3 (28-11-2015)
Masu kwafar Rubutunmu suna chanza masa launi, Kuji tsoron Allah ku dena. wannan cin amanar ilimi ne. Kuma Allah zai tambayeku.
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support