Duniya makaranta !! (fitowa ta 24) dr.mansur ibrahim sokoto ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 25 July 2017

Duniya makaranta !! (fitowa ta 24) dr.mansur ibrahim sokoto

DUNIYA MAKARANTA

Fitowa ta 24

116. Makaho idan idonsa ya bude karya sandarsa yake yi. Wani ma kona ta zai yi da wuta. Haka dan Adam yake da saurin manta alheri da kin tuna baya. Duk wanda za ka taimake shi yi ma sa don Allah. Idan kana jiran godiya da sakayya daga mutane babu shakka za ka sha mamaki.

117. Wawa ne yake fadin abin da zai aikata. Mai kuri shi yake bayyana abin da ya aikata. Mai natsuwa aikinsa ne ke bayyana matsayinsa.

118. Gishiri da Sukari kalarsu daya ce. Banbancinsu yana bayyana ne idan aka dandana. Haka mutane su ke; sai an gwada akan san na kwarai.

119. Zama da mutanen kirki yana karar da kai ababe guda shida: Son Allah, da bin Allah, da ambaton Allah, da gudun duniya, da son lahira da barin giraman kai.

120. Har abada akwai zukatan da ke son ka ko da kana munana ma su. Akwai kuma ma su kin ka duk yadda ka kyautata ma su. Kowa da kiwon da ya karbe shi.

Rubutawa: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

28/10/1438
22/7/2017

» Gabatarwa Zauren Minbarin Malamai +2347037477743
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support