Duniya makaranta !! (fitowa ta 26) dr.mansur ibrahim sokoto ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 25 July 2017

Duniya makaranta !! (fitowa ta 26) dr.mansur ibrahim sokoto

DUNIYA MAKARANTA

Fitowa ta 26

126. Tsare gaskiya ba ya hana rayuwa jin dadi. Karya da zulanci da zulunci da cin amana ba su kawo samu.

127. Abu biyu idan kana da su kai Sarki ne: Lafiya da wadatar zuci.

128. Duk abin da ya sa ka damuwa idan ka yi nazarin sa ya taba sa ka murna. A duniya babu abin murna na din-din-din sai dai a aljanna.

129. Karamin yaro da Fensir yake rubutu. Idan ya girma sai ya koma ga Biro. Dalilin haka shi ne, kuskuren yaro mai saukin gogewa ne. Goge kuskuren babba kam akwai wahala gare shi.

130. Mutane iri biyu ne: Wani yana rayuwa ne don ya ci, wani kuma yana ci ne don ya rayu. Koka gane bambanci tsakaninsu?

Rubutawa: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

30/10/1438
24/7/2017

» Gabatarwa Zauren Minbarin Malamai +2347037477743
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support