Duniya makaranta !! (fitowa ta 29) dr.mansur ibrahim sokoto ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Thursday 27 July 2017

Duniya makaranta !! (fitowa ta 29) dr.mansur ibrahim sokoto

DUNIYA MAKARANTA

Fitowa ta 29

141. Idan kana son ganin yadda duniya za ta kasance a bayanka, ka duba yadda take a bayan mutuwar wani irinka. Za ka ga yadda masoya ke manta masoyansu, rigima ta harde tsskanin magadansu wanda bai manta ka kawai shi ne Allah mahaliccinka. Manta da kowa ka nemi yardarsa.

142. Wand ba sallah an harmata ma sa jin dadin duniya, kuma zai gamu da wahalhalu a wurare guda hudu: A nan duniya, da ranar mutuwa, da cikin kabari da ranar hisabi.

143. A nan duniya ana debe ma sa albarka, a cire ma sa kwarjini daga fuska, a sa ma jama'a kyamar sa.

144. A ranar mutuwa zai mutu da wulakanci da yunwa da kishirwa.

145. A cikin kabari Allah zai kuntata ma sa, a hasa ma sa wuta a cikin sa, a aika ma sa kurmarci a tsakanin fatar jikinsa da namansa.

146. A ranar hisabi za a bakanta fuskarsa, a yi masa hisabi dalla dalla, sannan a hada shi da Zabaniyawa da za su wurga shi cikin wuta.

a. Ya kai dan uwa mai sallah ka gode ma Allah q kan ni'imar da kake cikin ta da wadda za ka shiga a cikin a bayan mutuwarka.

Rubutawa: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

3/11/1438
27/7/2017

» Gabatarwa Zauren Minbarin Malamai +2347037477743
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support