Madigo da luwadi ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 8 July 2017

Madigo da luwadi

*MADIGO DA LUWADI*
.
.
*DAGA ZAUREN*
.
*KITABU WAS SUNNAH*
.
.
*ﻣﺠﻠﺲ ﺍﻟﺘﻌﻠﻴﻢ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ*
📓📔
Watsaps
08036222795
08136182627
.
.
*LECTURE METAKEN*
*MADIGO DA LUWADI 1*
.
15-10-2015
.
_Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuh_
.
_Topic of discussion dinmu yau in sha Allahu ta'ala shine babban annobar data kunno kai a wannan zamani wato "homosexuality and lesbianism" Duk da dai cewar ba baqon abu bane amma sai dai muji labarinsa a wasu qasashe can yau da gobe munaji sai a abun ya shigo mana Kafin muyi nisa cikin darasin zanso musan ma'anar homosexuality and lesbianism in brief suna nufin saduwar jinsi_
.
_Homosexuality shine saduwar namiji danamiji lesbianism shine saduwan mace da Mace: Wal'iyazubillah!!! ALLAH YA TSAREMU DA ZURIA BAKI DAYA AMEEN_
.
_Ammadai Yar,uwa inaso kisani shifa madigo ko luwadi babban zunubine sosai amusulinci Wanda zamu iya cewa idan aka cire shirka da kafirci toh yana iya biyo baya_
.
_Sannan kuma hukuncin wannan mummunan aikin wato madigo da luwadi yana kusan daidaine da hukuncin mutuminda yazagi manzon Allah_
.
.
_Kamar yanda mukasani shi Wanda yazagi annabi koda yatuba dolene bamakawa sai ankasheshi_
.
_Toh shima Dan luwadi da Yar madigo muddin yabari aka kamashi tabbas koda yace yatuba sefa anyimai hukuncin kuma zamuyi bayanin yanda ake hukunta masu wannan aikin insha,allahu_
.
.
_MANZON ALLAH SAW YACE:_
.
_MAFI GIRMAN ABUNDA NAKEJIN TSORONSHI AKAN AL,UMMATA SHINE AIKIN MUTANEN ANNABI LUD sahehu ibn majah 2077_
.
.
_Menene aikin mutanen annabi lud?_
.
_Shine dai madigo da luwadi_
.
_Allah yatsaremu_
.
_Awani hadisi so uku ajere manzon Allah yana tsinema Wanda yake aikata irin aikin mutanen Annabi lud_
.
_Manzon Allah (S.A.W) yace: ALLAH YATSINEMA WANDA YAKE AIKATA IRIN AIKIN MUTANEN ANNABI LUD, ALLAH YATSINEMA WANDA YAKE AIKATA IRIN AIKIN MUTANEN ANNABI LUD, ALLAH YATSINEMA WANDA  YAKE AIKATA IRIN AIKIN MUTANEN ANNABI LUD Aduba musnad na imam Ahmad mujalladi na daya hadisina 309 Imam Hakim annaisaburi yafitarda hadisin cikin mujalladi na Hudu hadisina 356_
.
_Imamul baihaki mujalladi na takwas hadisi 23_
.
_Kuma Ahmad shakir yace hadisine sahehi_
.
_Allah madaukakin sarki yatsaremu_
.
_Har ila yau manzon Allah yace:_
.
.
_DUK WAYANDA KUKA SAMESU SUNA AIKATA IRIN AIKIN MUTANEN LUD TOH KUKASHE MEYI DAKUMA WANDA AKEYI DASHI Ahmad shakir da muhammad nasiruden albani sun inganta wannan hadisin_
.
_Awani wajen kuma manzon Allah cewa yayi: ALLAH BAYA KALLON NAMIJINDA YAKE SADUWA DA NAMIJI KOKUMA MIJINDA YAKE SADUWA DA MACE TA DUBURA_
.
.
_Allah yatsaremu_
.
_Wato yan,uwa hadisai sunada yawa inada aketayin mummunan tanadi na bala,I da musiba ga wayanda suke aikata madigo da liwadi_
.
_Sedai acikin hadisan anasamun masu rauni dama hadisan karya_
.
.
_Amma dai koba komai ai asara da tabewa tagama tabbata akan mutuminda manzon Allah yajeramai tsinuwa harguda uku akanshi_
.
_Allah yatsaremu_
.
_Awani hadisi akace: DUK WANDA YAKEYIN LUWADI IDAN YAMUTU KO TAMUTU BATAREDA YA TUBABA TOH ACIKIN KABARINSHI ZA,A CHANJA SURARSHI IZUWA KAMANNIN ALADE_
.
_Sedai Allam ibnul jauzy yace wannan hadisin karyane betabbataba Daga manzon Allah SAW Yafitardashi acikin littafinsa mesuna AL MAUDU,AT mujalladi na uku hadisina 113_
.
_Ammadai yan,uwa koda wannan hadisin be ingantaba ammadai tabbas akwai abun firgici acikinshi kuma lallai yakamata muji tsoton Allah mukiyaye_
.
_Shekhul Islam Ibn Taimiya yace:_
.
_Sahabbai basuyi sabaniba akan cewa duk Inda akasamu meyin luwadi ko madigo toh kasheshi za,ayi walau shine yake yi kokuma akanshi akeyi sedai sunyi sabani akan irin kisanda za,ayi_
.
_Wasu sukace jefeshi da duwatsu za,ayi_
.
_Wasu sukace  Aa sama za,ahau dashi aratayeshi awajenda yafi ko ina tsawo agarin_
.
_Wasu sukace konashi za,ayi dawuta_
.
.
_Dan,uwa yanzu cikin ukunnan duk Wanda akayi wannene mesauki aciki??_
.
.
_Allah dai yatsaremu_
.
_Bari kuji irin taka tsantsan na magabata akan tsoronda sukeji akan madigo da luwadi_
.
_Watarana Safiyanu Sauri yashiga ban daki Sega wani yaro me kyawun fuska yashigomai_
.
_Safiyanu yace kuyi maza kufitarmin dashi dominkuwa Ni safiyanu inaganin atareda kowacce mace akwai shedan guda daya amma inaganin atareda duk wani yaro mekyau akwai  samada guda goma_
.
.
_Allah sarki kunji bayanin bayin Allah masu kaifin hankali_
.
_Amma Mu yanzu mukanmu munema shedanun_
.
_Allah madaukakin sarki yashiryamu_
.
.
_Bari muji wannan kissar_
.
.
_Daga Khalid bin Walid bin mugira Yarubuta takarda zuwaga sayyadina Abubakar  cewa yakama wani dan luwadi_
.
_Se Abubakar yanemi shawarar sahabbai akan Al,amarin Sayyadina Aliyu yace wannan babban zunubine Wanda kakaf duniya babu Wanda sukeyin irinshi face Al,umma guda daya tal sune mutanen Annabi lud kuma munsan irin hukuncinda Allah yayi musu  don haka ra,ayina shine akonashi da wuta se Abubakar yarubutama Khalid cewa yakonashi dawuta aikuwa take Khalid yasa aka hada wuta yakonashi_
.
_Aduba Attargib wat tarhib, mujalladi na uku shafina 289_
.
.
.
Allah yashiryar damu hanya madaidaiciya
.
.
Allah yatabbatarda duga diganmu akan tafarki irinna annabi da sahhabbai
.
.
```Jameel Alhassan Haruna Kabo```
_(Abu Khausar)_
.
Tareda
.
_Ameenatu M. Reemy_
.
Suka rubuta kuma suke mana fatan alheri semun hadu a bayani nagaba
.
.
.
Zaku iya samun shafinmu na facebook tawannan hanyar
https:/t/m.facebook.com/Kitabu-Wassunah-1522000298067561/
.
ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.

Subhanak Allahumma wabi hamdika nash hadu anla ila ha illah anta nastagfiruka  Wanatubu ilaika
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support