Goron sallah 7 daga (kitabu was-sunnah) ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Sunday 9 July 2017

Goron sallah 7 daga (kitabu was-sunnah)

*GORON SALLAH-7???!!!*
.
.
*DAGA ZAUREN*
.
*KITABU WAS SUNNAH*
.
.
*ﻣﺠﻠﺲ ﺘﻌﻠﻴﻢ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ*
📓📔
Watsaps
08036222795
08136182627
:
Yau 14-10-1438, wacce tayi dai dai da 8-7-2017***
:
Taken Lekca
.
*GORON SALLAH-7*
-
Wannan shine bayani na Bakwai
....
....
*ﺇﻥ ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ، ﻧﺤﻤﺪﻩ ﻭﻧﺴﺘﻌﻴﻨﻪ، ﻭﻧﺴﺘﻐﻔﺮﻩ، ﻭﻧﻌﻮﺫ ﺑﺎﻟﻠﻪ ﻣﻦ ﺷﺮﻭﺭ ﺃﻧﻔﺴﻨﺎ، ﻭﺳﻴﺌﺎﺕ ﺃﻋﻤﺎﻟﻨﺎ، ﻣﻦ ﻳﻬﺪﻩ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻼ ﻣﻀﻞ ﻟﻪ، ﻭﻣﻦ ﻳﻀﻠﻞ ﻓﻼ ﻫﺎﺩﻱ ﻟﻪ، ﻭﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺣﺪﻩ ﻻ ﺷﺮﻳﻚ ﻟﻪ ﻭﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻣﺤﻤﺪﺍ ﻋﺒﺪﻩ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ*
.
_Bayan haka abayani nabaya mun fara koro hadisai ne wayanda suke nuna mana falalar wannan ruwa na zam zam, yanzu kuwa zamu cigaba da ambata muku wayannan hadissan*****_
           _Akwai Wani hadisi na Abdullahi dan Abbas wanda yake cewa watarana Manzon Allah (s.a.w) yazo, semuka ebo masa guga guda ta ruwan zam zam yasa bakinsa yasha wannan ruwan sannan ya kurkure bakinsa da wannan ruwa na zam zam seya sake maidashi cikin wannan guga sai kuma sahabbai suka kar6i wannan guga suka juyeshi acikin rijiyar zam zam****_
        _Wato ruwan bakin Annabi wanda ya gwaurayashi da miyau na bakinsa sekuma ya watsashi acikin ragowan ruwanda yake cikin wannan guga Inji Abdullahi dan Abbas kafin suka kar6i wannan guga suka juyeta acikin rijiyar zam zam***_
_Idan mukayi la'akari da wannan hadisin kenan zamu iya cewa duk wanda yasha ruwan zam zam to yasha miyau na bakin Annabi muhammad (s.a.w) sannan kuma Annabi Yasa anzuba wannan ruwan gugan ne badan komaiba sesaboda Al'umarsa wayanda zasuzo bayansa suma su samu tabarrakinsa domin komai na jikin Annabi yanada albarka******_
        _Toh dama can ruwan zam zam yanada albarka amma yanzu kuma da aka watsa miyau na bakin Annabi acikinsa sekuma yaqara samun albarka****_
 _Ammafa ba dai dai bane abinda wayansu mutane sukeyi, sesu dinga shan ruwan Alwalan malamansu kokuma wani malami yayi khaki ya zubar se a dauka acinye wannan baki daya kuskurene, wayansuma Fitsarin malamin nasu sukesha, kaga wannan gangancine domin kuwa mutum ze iya shawoma kansa guloriya domin kuwa malaminku babu wanda yace yanada albarka, kuma bema fikaba domin qilama tana iya yiwuwa kai dinnan kafishi tsoron Allah kuma mafi falalar mutane awajen Allah shine wanda yafisu tsoronshi*****_
_Ibnu Sa'ad Acikin Addabaqatul Kubra yakawo wani labari na Ummu Aiman uwar goyon Annabi Muhammad (s.a.w) wacce take cewa Lokacinda Annabi (s.a.w) yake qarami beta6a yimata kukan yanajin yunwa ko yanajin qishiba, tace yakasance yanayin sammako da sassafe yatafi jikin ka'aba yasha ruwan zam zam yadawo kullun da safe yanayin haka, tace nikuma se inkawo mishi abinci amma seyace Aa na naqoshi banajin yunwa, kaga wannan labarin yana nuna mana cewa babban Abincin Annabi (s.a.w) asadda yake warami shine Ruwan Zam zam******_
_Toh gakuma Hadisin musulintar Abu zarri wanda yana cikin Sahihu Muslim, lokacinda Abu Zarri yashigo garin makka yadinga yawo yanaso yaga Annabi Muhammad ba tareda ya tambayi kowaba, ahaka yayita yawo anan cikin garin makka seda yakwashe kwanaki 30 a wannan gari na makka Yana yawo besamu haduwa da Annabi (s.a.w) kuma yanajin tsoro kada ya kira wani yatambayeshi wanene Annabi muhammad saboda yana tsoron kada a kasheshi tunda yasan irin yadda suke tsananin cutardashi da musulmai****_
          _Rannan kuwa Abu zarri yana zaune a gefen Ka'aba saiga Annabi (s.a.w) yazo, ya wuce har yaje ya sumbanci baqin dutse kuma yayi dawafi, taredashi akwai Sayyidina Abubakar, sannan yazo yayi dawafi, Abu Zarri yana ganinshi se ya gane cewa shine Annabi muhammad (s.a.w)****_
_Insha Allahu Bayani nagaba zamuji yadda takaya tsakanin Annabi muhammad (s.a.w) da Abu Zarri, sannan kuma zamuji ko meyene Alaqar wannan hadisin dakuma wannan lekca tamu*****_
:
:
Zamu dakata anan sekuma bayani nagaba Idan Allah yakaimu
=
=
_Almajirinku dan mutanen kabo_
'
_Jameel Alhassan Haruna Kabo_
_Alwahhaby-Assalafy_
.
 Nake mana fatan Alheri wassalamu alaikum
..
.
.
Zaku iya samun shafinmu na facebook tawannan hanyar
http://m.facebook.com/Kitabu-Wassunah-1522000298067561/
.
ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.

Subhanak Allahumma wabi hamdika ash hadu anla ila ha illah anta astagfiruka  Wa,atubu ilaika
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support