Masu hikima sunce ?? (fitowa ta 26) dr.mansur ibrahim sokoto ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 25 July 2017

Masu hikima sunce ?? (fitowa ta 26) dr.mansur ibrahim sokoto

MASU HIKIMA SUN CE

Fitowa ta 26

116. Zaman dan Adam a duniya kamar wata ne da haskensa. Idan hasken wata ya fara tun magariba har safe, to, hasken ya dinga raguwa kenan har mutuwarsa.

117. In dai jagabanka hankaka ne, to, kada ka yi kuka ina ya bi da kai hanyar mushe.

118. Wanda ya yi tsawon rai a duniya, zai ga abin da zai faranta masa rai, ya kuma ga abin da zai bakanta masa rai.

119. Komai dadin da ka ji a duniya, wadansu sun riga ka ji, sun kuma riga ka bari. Haka kai kuma za ka bar shi yadda suka bari.

120. Da ba ya jure ma wulakanci kamar yadda jaki da la'imi suke jure masa.


Littafin: Sheikh Baba Ahmad As-Shinkidi

Fitarwa da gyarawa: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

30/10/1438
24/7/2017

» Gabatarwa Zauren Minbarin Malamai +2347037477743
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support