YA DAMKE SHAITAN (L. A) Zauren fiqhu ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 29 July 2017

YA DAMKE SHAITAN (L. A) Zauren fiqhu

YA DAMKE SHAITAN (L. A)
***************************
Sayyiduna Abud Darda'i (ra) yace : "Manzon Allah (saww) ya mike yana sallah sai muka ji shi yana cewa:
"A'udhu bil Lahi minka" (Ina neman tsarin Allah daga sharrinka). Sai da ya fa'da sau uku. Sannan yace "INA TSINE MAKA DA CIKAKKIYAR TSINUWAR ALLAH". Ya fa'da har sau uku. Kuma ya bude hannunsa kamar yana kokarin damke wani abu.
Yayin da ya idar da sallar sai muka ce "Ya Ma'aikin Allah, hakika munji kana fa'din wani abu acikin sallah, wanda bamu ta'ba jin ka fa'di irinsa kafinsa ba. Kuma mun ga ka bude hannunka".
Sai Manzon Allah (saww) yace: "HAKIKA IBLEES MAKIYIN ALLAH, YAZO DA GARWASHIN WUTA ZAI SANYASHI A FUSKATA, SAI NACE MASA "INA NEMAN TSARIN ALLAH DAGA GAREKA" HAR SAU UKU, SANNAN NACE "INA TSINE MAKA DA TSINUWAR ALLAH CIKAKKIYA".
AMMA DUK DA HAKA BAI JA DA BAYA BA. HAR SAU UKU. SANNAN SAI NAYI NUFIN IN DAMKESHI.
WALLAHI BA DON ADDU'AR 'DAN UWANMU (ANNABI) SULAIMAN (AS) BA, DA SAI SHI (IBLEES DIN) YA WAYI GARI A DAURE, YARAN MUTANEN MADEENA SUNA WASA DASHI".
Imamu Muslim ne ya fitar da hadisin acikin Kitabul Masajid, Juzu'i na 1 shafi na 385.
DARASI
********
Darussan dake cikin wannan Mu'ujizar sun hada da :
1. Taurin kai da rashin mutunci irin na Iblees. Ku dubi yadda Manzon Allah (saww) ya nemi tsarin Allah daga sharrinsa amma bai ja da baya ba.. Sannan ya tsine masa har sau uku amma bai ja da baya ba.
Wannan yana nuna mana cewar lallai Iblees (L. A) ba Qaramin shu'umi bane. Ya Allah ka kiyayemu daga sharrinsa.
2. Halaccin neman tsari daga sharrin shaitan yayin da kake cikin sallah, idan wani waswasi mai Qarfi ya bijiro maka. (musamman ga wadanda suke fama da matsalar shafar aljanu).
3. Fifikon Annabi Muhammadu (saww) a saman dukkan Annabawa (as). Domin babu wani Annabin da ya ta'ba damkar Iblees da hannunsa in ba Annabi Muhammadu ba (saww).
Ko shi Annabi Sulaiman (as) Allah ya hore masa shaitanun suna yin hidima agareshi. Amma bai ta'ba damkar shaitan da hannunsa ba.
4. Tawadhu'u irin na Annabi Muhammadu (saww) ku dubi yadda ya hakura ya saki shaitan din saboda tunawa da addu'ar wani 'dan uwansa daga cikin Annabawan Allah (as).
Ya Allah ka ninninka salati da girmamawa da aminci bisa Annabinmu Muhammadu tare da iyalan gidansa tsarkaka da Sahabbansa gwargwadon adadin kalmominka da dawwamar mulkinka Ya Rahman.
DAGA ZAUREN FIQHU
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support