Hukuncin yin aure akan aure ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Friday 7 July 2017

Hukuncin yin aure akan aure

HUKUNCIN YIN AURE AKAN AURE :
TAMBAYA TA 2245
********************
Assalamu alaikum malam da fatan kana lfiya? Allah ya bada lada.
Malam ina da tambya, yar uwa tace tayi aure, sai ta na da ciki wata 6 suka dan samu matsala mijin yace tàje gida ta haihu. Malam shekara goma kenan da dawowanta kuma ya hanata komawa kuma yayi aure ya kai sau uku. Malam ya matsayin auran nasu tunda ba sakin ta yayi ba kuma tace ita wani auran zatayi.
AMSA
*******
Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
A'a bai halatta gareta tayi wani aure ba. Domin har yanzu tana nan amatsayin Matar shi wancan Mijin nata tunda bai ce ya saketa ba.
Abinda ya kamata tayi shine iyayenta da nashi su zauna atsakaninsu su daidaita tsakanin 'Ya'yansu. Idan kuma daidaiton ba zao yiwu ba, to sao a raba auren cikin Mutunci da Girmamawa.
Idan kuma duk ba'a samu Mafita ba, Ya kamata akai maganar nan gaban Alkali domin ya gudanar da bincike ya fidda hukunci atsakaninsu.
Shima Mijin bai yi daidai ba. Domin kuwa bai kamata mutum ya kyale Matarsa har tsawon shekara goma shi bai saketa ba, Kuma bai mayar da ita gidansa ba. Wannan ba daidai bane bisa doron karantarwar Alqur'ani da Sunnar Manzon Allah (saww).
Allah cewa yayi :
"KADA KU CHUTAR DASU DON KU QUNTATA GARESU. IDAN KUMA SUN KASANCE MASU JUNA NE, TO KU CIYAR AKANSU (WATO KU DAUKI NAUYINSU) HAR SAI SUN HAIFE CIKINSU".
Da fatan Allah shi daidaita tsakanin nasu idan hakan ne yafi alkhairi garesu. Tunda Allah yace : "SULHU ALKHAIRI NE".
Idan kuma rabuwar ce tafi alkhairi garesu, to dama don haka aka halatta yin saki din.
WALLAHU A'ALAM.
DAGA ZAUREN FIQHU
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support