Goron sallah 2 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Friday 21 July 2017

Goron sallah 2

*GORON SALLAH2???!!!*
.
.
*DAGA ZAUREN*
.
*KITABU WAS SUNNAH*
.
.
*ﻣﺠﻠﺲ ﺘﻌﻠﻴﻢ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ*
📓📔
Watsaps
08036222795
08136182627
:
Yau 14-10-1438, wacce tayi dai dai da 8-7-2017***
:
Taken Lekca
.
*GORON SALLAH-3*
-
Wannan shine bayani na Uku
....
....
*ﺇﻥ ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ، ﻧﺤﻤﺪﻩ ﻭﻧﺴﺘﻌﻴﻨﻪ، ﻭﻧﺴﺘﻐﻔﺮﻩ، ﻭﻧﻌﻮﺫ ﺑﺎﻟﻠﻪ ﻣﻦ ﺷﺮﻭﺭ ﺃﻧﻔﺴﻨﺎ، ﻭﺳﻴﺌﺎﺕ ﺃﻋﻤﺎﻟﻨﺎ، ﻣﻦ ﻳﻬﺪﻩ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻼ ﻣﻀﻞ ﻟﻪ، ﻭﻣﻦ ﻳﻀﻠﻞ ﻓﻼ ﻫﺎﺩﻱ ﻟﻪ، ﻭﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺣﺪﻩ ﻻ ﺷﺮﻳﻚ ﻟﻪ ﻭﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻣﺤﻤﺪﺍ ﻋﺒﺪﻩ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ*
.
_Bayan haka Inbaku mantaba acikin bayaninda ya gabata mun tsayane a inda Annabi Ibrahim (AS) ya dauko matarsa Hajara da Danta Isma'il wanda shekarunsa biyu a duniya a wannan lokacin seya kawosu wannan kwari wanda yake acikin dokar daji ya ajjesu, yajuya yakama gabansa zetafi, ananne ita hajara setabishi abaya, har yakai saman wani tudu inda ake cema saniyya seta qwala masa kira tace Ya Ibrahim yaya zaka kawomu wannan daujin kuna katafi kabarmu?? Shin Allah ne yace kayi hakan?? Seyace Eh Allah ne yace inyi hakan, sekawai tace to tafi abinka insha Allahu nasan Allah baze tozartamu ba*****_
          _Anan yakamata mudanyi ratse mujawo hankalin mazaje akan wayansu ababe guda biyu, na farko dai shine yanada kyau maza su sani cewa haqqine akansu su raba tsakanin matayensu musamman idan yazamana babu jituwa tsakanin matayen, wanda asalima shine ba,a hada mata guda biyu a gida daya batareda amincewarsuba, inhar zaka qara aure to lallai katanadarma kowacce gidan da zaka ajjeta, amma idan bazakayi hakanba to lallaine kafara neman yardarsu kafin kadasu inkuma daya tace bata yarda ka hadata gida da wata matar takaba, to lallai sedai ko kafasa auren kokuma kanema mata inda zata zauna, wannan shine farkon darasinda muka samu a wannan qissa ta Dauke hajara da Annabi Ibrahim yayi ya rabata da Uwargida Sarah***_
              _Abu nabiyu kuma shine mazaje suzama sun sabawa matarsu da gaskiya banda qarya, kunga dai irin wajenda Annabi Ibrahim yazo ya ajjiye Hajara wajene wanda yake dokar daji babu mutane awajen amma dayake yasaba mata da gaskiya dakuma tsoron Allah, tanaji yace Allah ne yace yakawota shikena  babu musuba gaddama ta amince, shin kadauka kaine hakan tafaru da kai shin kana tsammanin cewa matarka zata yarda dakai bazata qaryatakaba saboda tasan halinka????_
          _Saboda haka yanada kyau muzama masu gaskiya a zamantakewarda mukeyi da matayenmu kada musaba musu da qarya kuma mudena daukarwa kanmu abinda mukasan cewa bazamu iyaba****_
_Kuma wannan yana nuna mana muhimmancin barin mata suyi karatun Addini sufahimci girman Allah yadda zasu dinga mutunta al'amarin ubangiji yadda bazata kasance tanada za6iba aduk wani al'amrinda aka sanya ubangiji acikinsa*****_
             _Toh bayan Hajara takoma can wajenda ya ajjiyeta, shikuma Annabi Ibrahim yahau saman tsauni seyafadi wannan addu'ar wacce tazo acikin Suratul Ibrahim Ayata 37:_
*ﺭَﺑَّﻨَﺎ ﺇِﻧِّﻲ ﺃَﺳْﻜَﻨْﺖُ ﻣِﻦْ ﺫُﺭِّﻳَّﺘِﻲ ﺑِﻮَﺍﺩٍ ﻏَﻴْﺮِ ﺫِﻱ ﺯَﺭْﻉٍ ﻋِﻨْﺪَ ﺑَﻴْﺘِﻚَ ﺍﻟْﻤُﺤَﺮَّﻡِ ﺭَﺑَّﻨَﺎ ﻟِﻴُﻘِﻴﻤُﻮﺍ ﺍﻟﺼَّﻠَﺎﺓَ ﻓَﺎﺟْﻌَﻞْ ﺃَﻓْﺌِﺪَﺓً ﻣِﻦَ ﺍﻟﻨَّﺎﺱِ ﺗَﻬْﻮِﻱ ﺇِﻟَﻴْﻬِﻢْ ﻭَﺍﺭْﺯُﻗْﻬُﻢْ ﻣِﻦَ ﺍﻟﺜَّﻤَﺮَﺍﺕِ lﻟَﻌَﻠَّﻬُﻢْ ﻳَﺸْﻜُﺮُﻭﻥَ ‏( 37 ‏)*
*YA UBANGIJINMU! LALLAINE NI, NA ZAUNARDA WASU DAGA CIKIN ZURIYATA AWANI KWARI WANDA BABU SHUKA A WURIN DAKINKA ME ALFARMA. YA UBANGIJINMU! DOMIN SU TSAYARDA SALLAH SEKUMA KA SANYA ZUKATA DAGA MUTANE SUNA GAGGAUWAR BEGEN ZUWA GARESU, KUMA KA AZURTASU DAGA 'YA'YAN ITACE MEYIWUWA NE SURIQA GODEWA****
:
:
Zamu dakata Anan sekuma bayani nagaba Idan Allah yakaimu
=
=
_Almajirinku dan mutanen kabo_
'
_Jameel Alhassan Haruna Kabo_
_Alwahhaby-Assalafy_
.
 Nake mana fatan Alheri wassalamu alaikum
..
.
.
Zaku iya samun shafinmu na facebook tawannan hanyar
http://m.facebook.com/Kitabu-Wassunah-1522000298067561/
.
ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.

Subhanak Allahumma wabi hamdika ash hadu anla ila ha illah anta astagfiruka  Wa,atubu ilaika
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support