Goron sallah 2 daga (kitabu was-sunnah) ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 8 July 2017

Goron sallah 2 daga (kitabu was-sunnah)

*GORON SALLAH2???!!!*
.
.
*DAGA ZAUREN*
.
*KITABU WAS SUNNAH*
.
.
*ﻣﺠﻠﺲ ﺘﻌﻠﻴﻢ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ*
📓📔
Watsaps
08036222795
08136182627
:
Yau 13-10-1438, wacce tayi dai dai da 7-7-2017***
:
Taken Lekca
.
*GORON SALLAH-2*
-
Wannan shine bayani na Biyu
....
....
*ﺇﻥ ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ، ﻧﺤﻤﺪﻩ ﻭﻧﺴﺘﻌﻴﻨﻪ، ﻭﻧﺴﺘﻐﻔﺮﻩ، ﻭﻧﻌﻮﺫ ﺑﺎﻟﻠﻪ ﻣﻦ ﺷﺮﻭﺭ ﺃﻧﻔﺴﻨﺎ، ﻭﺳﻴﺌﺎﺕ ﺃﻋﻤﺎﻟﻨﺎ، ﻣﻦ ﻳﻬﺪﻩ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻼ ﻣﻀﻞ ﻟﻪ، ﻭﻣﻦ ﻳﻀﻠﻞ ﻓﻼ ﻫﺎﺩﻱ ﻟﻪ، ﻭﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺣﺪﻩ ﻻ ﺷﺮﻳﻚ ﻟﻪ ﻭﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻣﺤﻤﺪﺍ ﻋﺒﺪﻩ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ*
.
_Bayan haka In baku mantaba abaya mun tsayane Inda Wannan Azzalumin sarki ya sauka daga wannan qa'idar tashi, wato asali munce dama baya kama wacce batada miji, to amma yadda tsabar kyawu na Sarah ya tafiyarda tunaninsa duk da cewa ta manyanta amma take wannan sarki yakama sarah dukda cewa tagaya mishi cewa Annani Ibrahim (As) dan uwantane ba mijintaba****_
             _Alokacinda sarkinnan ya kadaita da ita a daki babu kowa dagashi se ita, se kawai yamiqa hannunsa ze kamota, inda nan take hannayensa suka bushe yazamana baya iya sarrafasu, ganin haka tasa wannan sarkin ya roqi sarah akan toyi masa Addu'a hannun nashi sukoma daidai, itako nan take setayi Addu'a, tana yin addu'ar se hannayen nashi suka koma daidai****_
           _Amma dayake dan Adam butulu ne seyasake yunquri a karo nabiyu yasake kai hannu ze kamata nanma dai hannun nashi suka qara maqalewa, seda akayi hakan har sau uku hannayen nashi suna shanyewa***_
              _Ganin wannan al'amarine yasa wannan sarkin ya fusata seya kira shugaban wayannan jami'ai nashi wayanda suke kamo masa mataye, yace dan mene zaka kawo min irin wannan matar???****_
            _Awannan lokaci se wannan sarki ya tsorata qwarai ya razana da Al'amarin Sarah, se yayi mata kyautar wata kuyanga mesuna Hajara, saboda dai yanaso dai a rabu lafiya kada wata matsala ta qara samunshi*****_
            _Bayan Annabi Ibrahim (AS) sun cigaba da tafiya sun isa qasar Falasdin se ita Sarah tabashi kyautar wannan kuyanga wacce wannan mugun sarki yabata kyautarta wato hajara, shikuma Annabi Ibrahim seyayi Sadaka da ita, wanda awannan lokacin har ita Hajara ta dauki ciki, wanda awannan lokacinne sekuma Kishi yakama Sarah, kasantuwar sun kwashe shekaru masu yawa suna tareda Annabi Ibrahim ita bata dauki cikiba****_
_Ana cikin haka sai wannan baiwa Hajara ta haihu wanda aukuwar hakan yasan kishi ya tsananta qwaqarai ta 6angaren uwargida Sarah tana ganin yaza,ayine daga zuwan wannan baiwa se kawai ta haihu alhalin ita e suke tareda Annabi Ibrahim tun suna quruciya amma ita bata haihuba****_
           _Wannan yasa ita Saratu take yiwa Hajara barazanar cewa zata Daddatsa ta kamar Yadda Ibnu Hajar ya Ambata acikin Fathul bari*****_
         _Wannan yasa ita hajara setaji tsoro,seta samu wani zani take daurawa ajikinta wanda shi zanin yanada jela ita kuma jelar zanin tana jan qasa, dan haka yakasance setake tafiya tana bin rerayi duk inda ta taka to wannan jelar zanin nata zeshare sahunta tana yin hakane saboda kada saratu tagane inda take, wato tana 6oyewa kenan, wanda malaman tarihi sukace Itace tafara yin dammara wanda mata sukeyi, wato alokacin wannan 6oye 6oyenda takeyi shine tayi wannan dammarar ajikin zaninta wannan yasa tazama mace tafarko da tafara yin dammara****_
           _To shikuma Annabi Ibrahim sa'adda yaga halinda Ita hajara tashiga ciki shine seya yanke shawarar ya dauketa daga nan wajen yakaita wani waje na daban, to shine sai kuma Allah yayi masa wahayin cewa yakaita can wani kwari, adokar daji wanda babu komai acikinsa face duwatsu da kwazazzabai****_
_To da wannan umarni hakanan Annabi Ibrahin yadaukota itada wannan dan nata Isma'ila wanda awannan lokacin baifi shekaru biyuba a duniya, amma Annabi Ibrahim hakana ya ajjesu awannan kwazazzabo wanda babu shuke shuke acikinsa kamar yadda Allah ta'ala ya labarta mana hakan acan cikin suratul Ibrahim*****_
:
:
Zamu dakata Anan sekuma bayani Nagaba Idan Allah yakaimu
=
=
_Almajirinku dan mutanen kabo_
'
_Jameel Alhassan HarunaY Kabo_
_Alwahhaby-Assalafy_
.
 Nake mana fatan Alheri wassalamu alaikum
..
.
.
Zaku iya samun shafinmu na facebook tawannan hanyar
http://m.facebook.com/Kitabu-Wassunah-152200029806y7561/
.
ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.

Subhanak Allahumma wabi hamdika ash hadu anla ila ha illah anta astagfiruka  Wa,atubu ilaika
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support