Yadda ake wankan janaba dana haila ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 3 January 2017

Yadda ake wankan janaba dana haila

*YADDA AKE WANKAN JANABA DANA HAILA*
.
.
*A ciki zamuga Bayanin Maniyyi da Maziyyi da Wadiyyi da Jinin haila* inkayi seka turama wani
:
DAGA ZAUREN
*Khulafa'ur-rashiidun*
:
Lucture 8
.
Muna me farawa da sunan ALLAH m rahama me jinqai, Tsira da amincin ALLAH su tabbaga ga shugaban halitta Annabi Muhammad (ﷺ).  Tare dashi da iyalansa da wadan da suka biyo bayan shi da kyautatawa irin au Sayyidina Abubakar, umar, usman, aliyu, dalha, zubair ibin auwam da sauran su.
;
A har kullum muna bada hakuri ga masu chanjamana  post suyi hakuri dan girman ALLAH kada ku chanja mana wannan post in, idan ka chanja ka cuci wanda ze karanta na gaba, ka hanashi  sauraron darasin baya dakuma nagaba wanda zamu gabatar da yaddan ALLAH,  Idan bazaka iya tura ma wani ba, ka hakura kada ka chanja mana post in mu dan ALLAHU.
°°°°°°°°°°°
*
*BABBANCHI TSAKANIN MANIYI DA MAZIYI DA WADIYI, DA RUWAN CIWON SANYI!!*
*
🚩MANIYYI-Yana fita ayayin babban sha'awa, kokuma ta hanyan mafarki, ko saduwa,ko wasa da Al-aura, kalan shi fari ne, yana da kauri sannan yana dan wari haka,  yayin fitan shi yana tunkudan juna, inyafiata kuma yana sa kasala./ kalan maniyin mace  yana daukeda launin yellow.
:
🚩MAZIYYI-wani kalan ruwan ne shima dayake fitowa daga Al-aura yayi qaramar sha'awa, maziyyi baida kauri yana nan da yaukie, yana fita yayina baligi yafara tinanin kusantan mace komace tayi sha'awa  namiji, idan ya fito tsarki kawai akemar sannan a wanke gurin.
:
🚩WADDIYI- Wani ruwa ne makaman cin maniyyi amma baya fita se bayan mutum ya girma wato ya tsufa, yawanci kuma yafi fitowa bayan gama fitsari
:
🚩CIWON SANYI-  wani ruwa ne me kauri da wari-wari dayake kwaranya kullum a farjin mata,  batare da wani sha'awa ba, kalan shi yakusa kama da maniyyi, yana fitane sanadiyan cuta, shi wannan yana buqatan inmace ta gani taje asibiti a bata magani!!
🚩
JININ HAILA
*
HAILA
     Shine wani jinin dake fita a farjin mace alhani lafiyarta qalau ba haihuwa tayi ba. Kuma ba kwanciya da wani na miji da yafi qarfinta ya fasa ta ba. Toh wannan shine jinin HAILA.
*
*
Duk sanda aka ga jini a farjin 'ya mace mai shekaru 7,8,9,10,12 ba tare da wani matsala a farjinta koh mahaifarta ba, ba kuma wani na miji da dafi qarfinta ya fasa ya ba toh wannan za abashi hukuncin jinin HAILA.
*
*
Balagar mace yana da alaqa da irin wajan da take rayuwa, yanayin halittar, jin dadinta. Shiyasa wasu suke fara jinin HAILA da wuri wasu koh nasu yake jinkiri.
*Misali;  Mazauna qasashen yammacin duniya inda akwai zafi baza a hada su da wurare irin su qasashen Russia da Afganistan ba sabo da wajene mai sanyin gaske.
.
.
Haka kuma mata masu cin abubuwan gina jiki da 'ya'yan itatuwa dole yanayin jinin su ya bambamta da na wa'yanda basu samu damar cin wa'yannan abubuwa ba.
.
.
LAUNUKAN JININ HAILA
*
(1) BAQI:
      (ba ana nufin baqi kalar gashi ba) ana nufin Ja mai duhu tare da qarni
   [Imam Abu dawud Nisa'e, Imam daru kudini, Ibn Hibban acikin sahihu muslim]
*
*
(2) JA JAWUR A
        Shine asalin launin jini. Yana dauke da qarni
*
*
(3) FATSE- FATSE
        (Kamar gwaiduwar kwai)
*
*
(4) RUWAN QASA
        Yana nan ne kamar qasa da aka kwaba da ruwa., yana da dan duhu duhu.
:
🚩KWANA KIN HAILA
.
.
Kwana kin haila ba a gayyade adadin sa, galibi wasu mata basa wuce kwana 5 zuwa 7 sai dai-daiku daga cikin su da suke zarce hakan.
.
.
ALAMUN DAUKEWA JININ HAILA
*
*Bushewar fargi qarqaf
        Idan farji ya bushe ba wani alama na jini koh kadan. Toh tsarki ya samu sai ayi wanka.
    Anaso a tanadi auduga mai kyau koh wani faril gyalle yadda za asa a farjin a duba domin tabbatar da tsarkakuwar
.
.
*CHANJAWAR KALAR JINI
   Mun riga munyi bayanin kalolin jini, Idan jinin hailarki baqi ne toh randa ya chanja kala ya koma Ja koh fatsi-fatsi bayan kuma kin cika adadin kwanakin da kika saba yi na hailar toh kin samu tsarki. Sai kiyi wanka ki ci gaba da ibadodin ki.
    SAI DE
       Idan wannan kalar jinin da ya chanje wato (istihada, ana qiran sa jinin ciwo koh jinin jijiya) bai dauke ba toh zaki riqa sake alwala a kowacce sallah, ki wanke inda jinin ma ya ta6a. Har sai sanda jinin ya dauke.
Amma idan ya fito bayan kin riga kin fara sallah toh shikenan ki ci gaba da sallarki.
*
🚩JININ BIKIE-/jinin haihuwa, shima kalanshi daya da na Haila, Sedai shimafi tsawon kwanakinshi shine kwana 60.
:
*MIYAKE WAJABTA WANKAN  JANABA?*
:
fitan maniyyi ta  kowacce hanya, in ma ta hanyan biyan buqata da matar ka, ko ta hanyar mafarki, ko kuma ta hanyan jin babban sha'awa da yayi sanadiyan fitan maniyi.
:
Shigar da kan kachiya cikin farji, yana wajabbata wanka koda kuwa baku fitar da maniyyi ba, wanka yawajaba agare ku.
:
Idan mace ta gama jinin Al-ada, da wance jinin haihuwa ya  dauke mata, wannan duka wajibi ne da suyi wanka.
*
Sekuma wankan shiga musulunchi, da wankan daukan harami. sannan se wankan gawa, gawanda ba'a filin yakie ya mutu ba, kokuma wanda ya qone sanadiyan gobara, ko lalacewan gaggan jiki. Sannan anso wanda yayi wankan gawa yayi wanka shima.
*
Wannan kusan sune wajiban wanka Da nasani.
:
*YA AKE WANKAN JANABA?*
*
Daga nana Aisha uwar muminai ALLAH yaqara mata yadda, tace:- "Manzon ALLAH(ﷺ) yakasance idan zaiyi wankan janaba, sai ya wanke  hannayen sa, sannan yayi wanka, sannan ya duddurza, ya tsattsefe gashinsa da hannayen sa, har inda ya tabbatar cewa ya jiqa fatar sa (kai) sai ya kwaranya masa (shi kan) ruwa sau uku, sannan ya wanke sauran jikn sa" tace;  na kasance ina yin wanka nida manzon  ALLAH (ﷺ) A kwary(baho) daya muna kamfata daga cikin ta baki daya"
(bukari da muslim)
:
_Dan uwa ka ta6ayin wankan janaba da matar ka bayan ta haihu sama da yara uku?  ina tinanin tinda kukayi lokacin kuna shekaran farko baku sake yiba_
*
Daga maimuna 'yar haris (R.A) matar Annabi (ﷺ) uwar muminai tace : "naje wajen Manzon ALLAH (ﷺ) da ruwan wanka janaba, sai ya  zuba ruwa da damansa aan hagunsa sau biyu k sau uku, sannan ya wanke hannunsa sau biyu ko sau uku, sannan ya wanke Al-auran sa, sannan ya daki qasa ko bango (in ba qasa a gefan ka zaka iya wanke hannunka da sabulu)  da hannun sa, sau biyu ko sau uku, sannan ya kurkure baki, ya shakie ruwa, ya wanke fuskar sa da damatsan sa, sannan ya kwaranya ruwa a bisa kansa, sannan y wanke jikinsa, sannan ya koma gefe ya wanke qafafunsa" tace " saina zo masa da kyalle (tawul) sai bai kar6e ba, sai ya riqa sharce ruwan da hannayen sa"
:
(Bukari da muslim)
:
_Anan zamu danyi bayani akan goge jiki da hannu, idan ka goge jikinka da hannu sekafi jin dadin wannan wankan, ba'a musu kusa da gida ka jarraba yauinkaje wanka koda kuwa bana janaba ba_
*
Wannan wanka👆🏽👆, haka akeyi idan mutum zeje sallan juma'a, idi, qarama ko babba, haka zalika anayi a wankan haila. idan kayi baka buqatan se ka sake Al-wala kawai sallah zakayi. sabda wankan karan kanshi Al-wala ne.
:
*YA AKE WANKAN HAILA?*
*
An karbo daga Aishata Allah Ya yarda da ita. Lallai Asma'a ta tambayi Manzon Allah (ﷺ)game da wanka haila, sai Yace: Dayarku ta dauki ruwanta da magaryarta tayi tsarki kuma ta kyautat tsarki sa'annan ta zuba ruwa a kanta, kuma ta cuda shi.., cudawa mai tsanani har sai ta sadar da ruwa ga asalin gashinta (tushen sa) sa'annan ta game jikinta da ruwa, sa'annan ta sami wani yanki na auduga mai kanshi ta tsarkaka da ita.
Sai Asma'a tace: Ya ya zata tsarkaka da ita? Sai Manzon Allah (ﷺ) yace: Subhanaallah! Nace tayi tsarku da ita. Sai Aisha tace: Kamar ita (Asma'a) tana boye wannan. Tace ma ta, "Abinda Annabi  (ﷺ)yake nufi shine ki bi gurbin jinin da ita.
:
(Malamai sun hadu akan shi)
*
Batare da tsawai tawa ba idan mace tana jinin haila bayan ta qare zatayi wanka, to wajibi ne akan ta da ta war ware gashin kanta kaman yadda hadisi ya tabbata a bukari hadisi na317  da Annabi (ﷺ) yace ma nana Aisha ta koma ta dakko miqati sannan ta warware gashinta..
:
An fani da magarya da miski  ba qaramin amfani yake dashi ba wajen taimakawa mace,  ki jarraba  baiwar ALLAH.
;
Dangane da wadan da jinin janaba ta same su a lokacin suna jinin Al-aada,  Abinda yafi shine tayi wanka biyu, daga janaba tasameta tayi wankan janaba, sanna idanjini ya dauke tayina haila. Wallahu a,alamu.
;
HARAMCHIN YIN WANKA DA RAGOWAN RUWAN WANKAN DA WANI YAYI AMFANI DASHI.
:
hadisi Sahihi  ya tabbata a cikin  littafin Bulugul maram Annabi ya hana wanka da ragowan ruwan wankan da wani ya rage haka ya hana wanka da ragowan ruwan mace"
*
 A hadisin dake jikin shi kuma an rawaiyo Annabi (ﷺ) yayu wanka da ragowan ruwan wankan matar shi maimuna":/
:
Wannan kusisiyace ta Annabi muhammad (ﷺ)   amma kai bai halatta kayi wanka da ragowan ruwan wankan matarka ba koitatayi da na ka.  Amma ba laipi kuyi wanka tare.
:
********
Idan ka sanar da wani kaima kayi da'awa kuma kayi taimakekkeniya akan biyayya wa ALLAH, Abin da mamaki sosaiakwai wadanda basu sani ba, yakamata kaisar musu,  sedai a kiyayi turawa  a groups inda suke da Dokan hana tura post, idn ka turabaka cire ka, kai kaso.
;
ANAN ZAN DAKATA  SE KUMA IN ALLAH YAKAIMU WANISHIRIN KUMA,  IDAN ALLAH YASO ZAMUYI BAYANI AKAN YADDA AKE WANKAN GAWA IN SHA ALLAHU
-------***-----------
MUHAMMAD AUWAL ABU JA'AFAR AL-POTISKUMAWI
•°°°°°°°°•
02/01/1438-03-10/2016
_________________
masu buqatan kasancewa damu, se su turo da suna da kuma sunan qasar su, a daure ayimana sallama cikakka dan samun lada cikekke.
*
→ MasU buqatan kasan cewa damu a whatsapp.
+2347035269582
+2348063796175
 tare da cikakken suna da kuma cikakkiyar sallama. don samun karatuttukan mu a facebook, saikubi, mobile.facebook.com/Khulafaur-Rashiidun-1812718708973541/ Subhanak Allahumma wabi hamdika Nash hadu anla ila ha illah anta nastagfiruka
Wana tubu ilaik.
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support