Goron sallah 6 (kitabu was-sunnah) ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 8 July 2017

Goron sallah 6 (kitabu was-sunnah)

*GORON SALLAH-6???!!!*
.
.
*DAGA ZAUREN*
.
*KITABU WAS SUNNAH*
.
.
*ﻣﺠﻠﺲ ﺘﻌﻠﻴﻢ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ*
📓📔
Watsaps
08036222795
08136182627
:
Yau 14-10-1438, wacce tayi dai dai da 8-7-2017***
:
Taken Lekca
.
*GORON SALLAH-6*
-
Wannan shine bayani na Shida
....
....
*ﺇﻥ ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ، ﻧﺤﻤﺪﻩ ﻭﻧﺴﺘﻌﻴﻨﻪ، ﻭﻧﺴﺘﻐﻔﺮﻩ، ﻭﻧﻌﻮﺫ ﺑﺎﻟﻠﻪ ﻣﻦ ﺷﺮﻭﺭ ﺃﻧﻔﺴﻨﺎ، ﻭﺳﻴﺌﺎﺕ ﺃﻋﻤﺎﻟﻨﺎ، ﻣﻦ ﻳﻬﺪﻩ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻼ ﻣﻀﻞ ﻟﻪ، ﻭﻣﻦ ﻳﻀﻠﻞ ﻓﻼ ﻫﺎﺩﻱ ﻟﻪ، ﻭﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺣﺪﻩ ﻻ ﺷﺮﻳﻚ ﻟﻪ ﻭﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻣﺤﻤﺪﺍ ﻋﺒﺪﻩ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ*
.
_Bayan haka In ba'a mantaba abaya munji irin tsawon shekarunda aka kwashe ana  amfani da Ruwan zam zam wanda duk fadin garin makka babu rijiya Zam zam kawai shine daya dayan ruwa wanda suke amfani dashi, kuma ba,a ta6a samun wani lokaci wanda aka nemi wannan ruwan aka rasa ba****_
               _Kuma komai haqarda zakayi awannan garin bazaka samu ruwaba, gashi qasashe dadama sukan tura musamman aje wannan qasa da jarkoki ayo musu safarar ruwan zam zam, wanda mukuma anan qasar hausa yana daga cikin Dimuwarda ta samemu shine mutum zebar garinsu yatafi makka amma sekaga yanayo muku tsarabar wata bagaruwa ko wata tsummar jallabiya, amma sekaga babu ruwan zam zam acikin tsarabar tashi, kaga wannan babu shakka dimuwa ce ta samemu, ai malam idan kasamu ka isa wannan gari to babban abinda zakayowa mutane tsarabarshi babu fa kamar Ruwan zam zam, amma dai kucigaba da binmu da sannu zakuji meyasa nace Zam zam shine yafi dacewa kuyowa mutane tsarabarshi*****_
              _Akwai Hadisi wanda Abdullahi dan Abbas da Abdullahi Dab Umar suka ruwaito wanda Annabi (s.a.w) yace: RUWAN ZAM ZAM  WANI IDO NE DAGA IDANUN RUWAN ALJANNA***_
          _Wannan shine yasa malamai suke cewa mutuminda yasha Ruwan Zam zam idan da ze rantse cewa yasha ruwan Aljanna to bazeyi kaffara ba, Kakoga aiko wannan kadai ya isa yazama hujjarmu tacewa Zam zam shine abinda yafi dacewa kayowa mutane tsarabarsa dankuwa yanada babbar albarka kuma duk wanda kabashi zam zam yasha to ruwane kabashi daga cikin ruwayen Aljannah***_
_Yazo a tarihi cewa sau hudu ana wanke zuciyar Annabi muhammad (s.a.w) da ruwan zam zam****_
       _Na farko shine lokacinda Annabi (s.a.w)yake wajen Halimatus sadiyya sannan yanada shekaru hudu a duniya, Hadisin yana Cikin sahihu Muslim, mala'iku suka sauko sukazo da wata tasa suka bude qirjin Annabi muhammad (s.a.w) suka ciro zuciyarsa suka wanketa da ruwan zam zam sannan suka maida ita suka rufe***_
             _Wanki nabiyu kuwa anyi masane a lokacinda ya cika shekaru goma da Haihuwa******_
                   _Wanki Na uku kuma shine lokacinda yacika Shekaru 40 a duniya sadda Jibrilu yafara kawo masa wahayi nanma seda aka wanke zuciyarsa da Zam Zam kafin aka fara yimasa wahayi, sedai wannan ruwayar ita akwai 'yan maganganun na malamai gameda ingancinta****_
                 _Na hudu kuma shine lokacinda Za,ayi Isra'i Mi'iraji dashi Allah yana buqatar ganinshi nanma seda aka kaishi dakin ka'aba mala'ika ya kwantar dashi aka wanke zuciyarsa da ruwan zam zam sannan aka kawo buraqa aka tafi dashi,  Wanna  hadisin Abu Zarri ne, wanda yake cikin Bukhari da Muslim*****_
_Kamar yadda na fada cewa bamaso mu tsawaita shiyasa bazamu riqa kawo larabcin hadisinba musamman dayake wayansu hadisan dogayene amma bari mudan yanko wani bangaren wannan na hudun kamar yadda yake dogone sosai acikin Bukhari:_
*ﻛَﺎﻥَ ﺃَﺑُﻮ ﺫَﺭٍّ ﻳُﺤَﺪِّﺙُ ﺃَﻥَّ ﺭَﺳُﻮﻝَ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺻَﻠَّﻰ ﺍﻟﻠﻪُ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﻭَﺳَﻠَّﻢَ ﻗَﺎﻝَ : "ﻓُﺮِﺝَ ﻋَﻦْ ﺳَﻘْﻒِ ﺑَﻴْﺘِﻲ ﻭَﺃَﻧَﺎ ﺑِﻤَﻜَّﺔَ، ﻓَﻨَﺰَﻝَ ﺟِﺒْﺮِﻳﻞُ ﺻَﻠَّﻰ ﺍﻟﻠﻪُ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﻭَﺳَﻠَّﻢَ، ﻓَﻔَﺮَﺝَ ﺻَﺪْﺭِﻱ، ﺛُﻢَّ ﻏَﺴَﻠَﻪُ ﺑِﻤَﺎﺀِ ﺯَﻣْﺰَﻡَ، ﺛُﻢَّ ﺟَﺎﺀَ ﺑِﻄَﺴْﺖٍ ﻣِﻦْ ﺫَﻫَﺐٍ ﻣُﻤْﺘَﻠِﺊٍ ﺣِﻜْﻤَﺔً ﻭَﺇِﻳﻤَﺎﻧًﺎ، ﻓَﺄَﻓْﺮَﻏَﻪُ ﻓِﻲ ﺻَﺪْﺭِﻱ، ﺛُﻢَّ ﺃَﻃْﺒَﻘَﻪُ، ﺛُﻢَّ ﺃَﺧَﺬَ ﺑِﻴَﺪِﻱ، ﻓَﻌَﺮَﺝَ ﺑِﻲ ﺇِﻟَﻰ ﺍﻟﺴَّﻤَﺎﺀِ ﺍﻟﺪُّﻧْﻴَﺎ*
_Awani Hadisin kuma Manzon Allah (s.a.w) yace: RUWAN ZAM SAM SHINE MAFI ALHERIN RUWA A BAYAN QASA ACIKINSHI AKWAI ABINCI WANDA YAKE QOSARDA MEJIN YUNWA, KUMA AKWAI MAGANI WANDA YAKE WARKARDA MUTUM DAGA DUKKAN CIWO****_
           _Babu wani ruwa a duniya wanda yafi zam zam alheri, sannan kuma zam zam abincine ga mutuminda yake jin yunwa, sannan kuma ga mara lafiya wannan ruwan maganine, ciwon kuma ko wanne irine matuqar ba tsufa bace ko mutuwa*****_
            _Wannan hadisin zamuzo muyi sharhinsa nangaba zakuji yadda mutane sukaita gwada amfani da wannan ruwa akan cututtukanda suke damunsu kuma suka samu waraka cikin yardar Allah****_
:
:
Zamu dakata anan sekuma bayani nagaba Idan Allah yakaimu
=
=
_Almajirinku dan mutanen kabo_
'
_Jameel Alhassan Haruna Kabo_
_Alwahhaby-Assalafy_
.
 Nake mana fatan Alheri wassalamu alaikum
..
.
.
Zaku iya samun shafinmu na facebook tawannan hanyar
http://m.facebook.com/Kitabu-Wassunah-1522000298067561/
.
ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.

Subhanak Allahumma wabi hamdika ash hadu anla ila ha illah anta astagfiruka  Wa,atubu ilaika
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support