Masu hikima sunce ?? ( fitowa ta 24) dr.mansur ibrahim sokoto ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 25 July 2017

Masu hikima sunce ?? ( fitowa ta 24) dr.mansur ibrahim sokoto

MASU HIKIMA SUN CE

Fitowa ta 24

106. Mai son duniya da lahira kamar mai mata biyu ne a duniya. Idan ya shirya da daya sai su bata da daya.

107. Iyakar dan Adam ya yi kokari bisa sha'anin duniyarsa, amma ba tilas ne duk sha'aninsa ya zo masa yadda yake so ba.

108. Ka girmama kanka don mutane su girmama ka. Idan kai ka wulakanta kanka faufu, babu mai girmama ka.

109. Idan zukatan masoya suka kusanci juna, nisan jiki ba ya raba su.

110. In dai kana da lura kwanakinka na duniya sa yi maka wa'azi, domin ba dayan su da zai wuce ka ba ka ga wani abin mamaki ba.


Littafin: Sheikh Baba Ahmad As-Shinkidi

Fitarwa da gyarawa: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

28/10/1438
22/7/2017

» Gabatarwa Zauren Minbarin Malamai +2347037477743
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support