Masu hikima sunce ?? (fitowa ta 25) dr.mansur ibahim sokoto ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 25 July 2017

Masu hikima sunce ?? (fitowa ta 25) dr.mansur ibahim sokoto

MASU HIKIMA SUN CE

Fitowa ta 25

111. Sau da yawa kakan ga wanda ya tara duniya ba shi ne mai cin ta ba. Kamar yadda ka kan ga wani ya cinye duniyar da ba shi ya tara ba.

112. Har mulkin Annabi Sulaimanu ya faru ya kare dare da rana suna nan yadda suke. Ballai ma wani.

113. Duk masifar da ta samu dan Adam yana jin ciwon ta. Amma ya fi jin ciwon dariyar da abokan gaba suke yi masa.

114. Hakikanin mai jin dadi a duniya shi ne wanda tubatuban zamani ba su same shi ba.

115. Idan ka yi gudun wani abin da Allah ya kaddaro maka, ka yi gudun banza. Inda ka sa fuskarka duk shi ne zaka taras


Littafin: Sheikh Baba Ahmad As-Shinkidi

Fitarwa da gyarawa: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

29/10/1438
23/7/2017

» Gabatarwa Zauren Minbarin Malamai +2347037477743
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support