Buhari ya matsu ya dawo gida – Gwamna Ortom ya yi Magana bayan ziyarar Landan ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Friday 28 July 2017

Buhari ya matsu ya dawo gida – Gwamna Ortom ya yi Magana bayan ziyarar Landan

- Gwamnan jihar Benue ya bayyana cewa shugaba Buhari na Allah Allah ya dawo Najeriya

- Samuel Ortom yabce shugaban kasar ya tambaye game da tsaro a jihar Benue

-Ya kuma bayyana cewa shugaban kasar zai dawo da zaran ya gama maganinsa a Landan

A ranar Alhamis, 28 ga watan Yuli, Gwamnan jihar Benue Samuel ya bayyana cewa shugaba Buhari na Allah Allah ya dawo Najeriya.

Ortom yace Buhari na Allah Allah ya dawo da zaran ya kammala maganinsa a Landan.

Ya kara da cewa shugaban kasar ya ji sauki sosai wanda yace alama ce ta cewa Allah na amsar adduóín miliyoyin ýan Najeriya kan halin da Buhari ke ciki.

Ya kuma ce Buhari ya yi barkwanci da gwamnonin da suka kai masa ziyara.

Ortom ya kuma bayyana cewa shugaban kasar ya nuna kulawa kan halin da tsaro ke ciki a jihar Benue da kuma yadda shi gwamnan ke magance su.
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support