M͟a͟s͟u͟ h͟i͟k͟i͟m͟a͟ s͟u͟n͟c͟e͟ (f͟i͟t͟o͟w͟a͟ t͟a͟ 17) ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Monday 17 July 2017

M͟a͟s͟u͟ h͟i͟k͟i͟m͟a͟ s͟u͟n͟c͟e͟ (f͟i͟t͟o͟w͟a͟ t͟a͟ 17)


MASU HIKIMA SUN CE

Fitowa ta 17

              2. WASICI
Ga wasicin Sarkin Musulmi Umaru dan Khaddabi da ya yi ma Sa'idu dan Wahabi, lokacin da ya nada shi Gwamna. Yace,

"Ya kai Sa'adu! Na shugabantar da kai a kasar Iraki. To, ka kiyaye wasiyyata. Kar ka rudu da cewa kai kawun Annabi ne, ko kai sahabinsa ne. Ka sani mummunan aiki ba ya wanke wani mummuna irin sa. Aiki na gari shi ne yake wanke mummuna. Ka sani Allah ba shi da zumunta tsakanin sa da bayinsa in ba ta bin sa ba. Ka ga mutane, mai darajarsu, da kaskantaccensu, wurin Allah duk daya ne. Shi Ubangijinsa ne, su kuwa bayinsa ne. Ka dubi al'amarin da ka ga Annabi yana a kan sa, tun ranar da aka aiko shi har ya zuwa rabon sa da mu, ka lazimce shi. Ka saba ma kanka da wanda ke tare da kai alheri, da shi za ka fara. Ka sani tsoron Allah yana cikin abu biyu ne; bin umurninsa da barin sabon sa. To, Allah ya kiyaye ka".

Littafin: Sheikh Baba Ahmad As-Shinkidi

Fitarwa da gyarawa: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

22/10/1438
16/7/2017

» Gabatarwa Zauren Minbarin Malamai +2347037477743
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support