Duniya makaranta !! ( fitotwa ta 30) dr.mansur ibahim sokoto ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Sunday 30 July 2017

Duniya makaranta !! ( fitotwa ta 30) dr.mansur ibahim sokoto

DUNIYA MAKARANTA

Fitowa ta 30

151. Wanda fuskar mata take ba shi sha'awa mata daya ba ta isar sa. Amma wanda kyakkyawan hali yake so daya ma sai ishe shi.

152. Idan kana cikin damuwa ka jira samun sauki daga wurin Allah, wannan jiran da kake yi ibada ne. Domin kyautata zato ne ga Allah. Wanda ya kyautata ma Allah zato kuwa lallai ne Allah zai ishe shi.

153. Duk lokacin da fitila ta yi sama haskenta ya fi yaduwa. Idan Allah ya daukaka ka, yi kokari ka zamo fitila mai kawar da duhu da damuwa daga mutane.

154. Urwatu bn Zubair, ya gamu da jarrabawar ciwon Cancer a kafarsa. Da magani ya gagara sai aka yanke shawara akan cire masa kafar ga baki daya. Amma a wannan dare bai fasa karanta abin da ya saba yi na Alkur'ani da Zikiran Ubangiji ba. Duhu gani, sau nawa ne karamar matsala ta durkushe ka daga ibada?

155. Kyawon hankali ya rika tunani. Kyawon harshe ya rika faadin gaskiya. Kyawon budurwa kunya. Kyawon Yaro biyayya.

Rubutawa: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

5/11/1438
29/7/2017

» Gabatarwa Zauren Minbarin Malamai +2347037477743
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support