Kwazazzabon wutur jahannama ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Friday 7 July 2017

Kwazazzabon wutur jahannama

KWAZAZZABON WUTAR JAHANNAMA
****************************************
Hakika Wutar Jahannama tana da kwarurruka da kwazazzabai da dama wadanda Allah ya tanadesu domin azabtarwa ga Kafirai da Fasikai da masu sa'bonsa.
Wasu daga cikin wadannan Kwazazzabai ambatonsu yazo acikin Alqur'ani, wasu kuma acikin hadisai. Wasu kuma ba za'a sansu ba. Sai dai wadanda suka shiga wutar su zasu gansu (Allah shi kiyayemu don karfin ikonsa).
1. WAILUN : Shine wanda ambatonsa yazo awurare da dama cikin Alqur'ani da hadisai.
Abu Sa'eed Alkhudriy (ra) yace Manzon Allah (saww) yace : "WAILUN WANI KWARI NE ACIKIN JAHANNAMA WANDA SAI KAFIRI YAYI SHEKARU ARBA'IN YANA WULWULAWA ACIKINSA KAFIN YA KAI QASANSA".
(Imamu Ahmad ne da Tirmidhiy suka ruwaitoshi).
Acikin wata riwayar ta Tirmidhiy cewa yayi "WANI RAMI NE ATSAKANIN DUWATSU BIYU (NA WUTA). KAFIRI KAFIRI ZAI YI SHEKARU SABA'IN YANA WULWULAWA ACIKINSA KAFIN YA KAI QARSHEN QASANSA".
Ibnu Hibban ma ya ruwaitoshi kuma Imamul Hakim ya ruwaitoshi kuma ya inganta Isnadinsa.
Daga cikin wadanda zasu shiga wannan ramin na "WAILUN" akwai :
- Masu wasa da sallah.
- Masu tauye Mudu ko Sikeli.
- Masu Qin fidda zakkah.
- Masu Qirkirar abu sannan su dangantashi da Allah.
- Masu Qirkirar labarai na Qarya don ayi dariya.
- Masu yin girman kai idan anyi musu Wa'azi.
2. SA'OOD : Shima ambatonsa yazo acikin suratul Mudatthir ayah ta 17.
Abu Sa'eed Alkhudriy (ra) ya karbo daga Manzon Allah (saww) yana cewa: "WANI DUTSE NE NA WUTA ZA'A TILASTASHI (SHI 'DAN WUTA) CEWA SAI YA HAURO SAMANSA. AMMA IDAN YA DORA HANNUNSA AKANSA SAI HANNUN YA NARKE.
IDAN KUMA YA DAUKE HANNUN SAI HANNUN YA DAWO. IDAN YA DORA QAFARSA AKANSA SAI QAFAR TA NARKE. IDAN YA DAUKETA SAI TA DAWO. SAI YAYI SHEKARU SABA'IN YANA HAWANSA KAMAR HAKA".
(Imamu Ahmad da Hakim ne suka ruwaitoshi kuma Hakim ya inganta isnadinsa).
Acikin riwayar Imamut Tirmidhiy kuma cewa yayi "ZAI YI SHEKARU SABA'IN YANA HAUROWA SAMANSA, KUMA ZAI YI KAMAR HAKA (SHEKARU SABA'IN DIN) YANA GANGAROWA.. HAKA ZAI YI HAR ABADA".
3. GAYYU : Ambatonsa yazo acikin Suratu Maryam (as) ayah ta 59.
Abdullahi 'dan Mas'ud (ra) yace "WANI RAMI NE ACIKIN JAHANNAMA WANDA CIKINSA AKE JEFA MASU BIN SHA'AWARSU". (WATO DUK WANDA YAKE BIYE MA SHA'AWA, AWANNAN RAMIN ZA'A JEFASHI IN BAI TUBA BA).
Imam Tabaraniy da Baihaqiy ne suka riwaitoshi.
Acikin wata riwayar daga Imamul Baihaqiy kuma cewa yayi "(GAYYU) WANI KOGI NE MAI TSANANIN ZURFI DA KUMA QAZAMIN DANDANO".
4. MAUBIQ: Acikin fassara ayar nan ta 52 acikin suratul Kahfi, (WA JA'ALNA BAINAHUM MAUBIQA). Sayyiduna Anas bn Malik (ra) yace "(MAUBIQ) WANI KOGI NE NA 'DIWA DA JINI".
(BAIHAQIY NE YA RUWAITO).
5. JUBBIL HUZNI (RAMIN BAQIN CIKI) : Shi kuma acikin hadisi ne ambatonsa yazo. Wato hadisin da Imamul Baihaqiy ya ruwaito daga Sayyiduna Aliyu bn Abi Talib (ra) shi kuma yaji daga Manzon Allah (saww) yana cewa:
"KU NEMI TSARIN ALLAH DAGA JUBBIL HAZNI".
Sai suka ce "Ya Rasulallahi menene Jubbul Huzni?".
Sai Annabi (saww) yace "WANI KWARI NE ACIKIN JAHANNAMA WANDA ITA KANTA JAHANNAMA A KULLUM TANA NEMAN TSARI DAGA SHARRINSA HAR SAU SABA'IN.
ALLAH YA TANADAR DASHI NE SABODA QARI'AI (WATO MAHADDATAN ALQUR'ANI) MASU YIN RIYA".
(Imamul Baihaqiy ne ya ruwaitoshi da isnadi mai kyau).
An karbo kusan irin wannan hadisin daga Sayyiduna Abu Hurairah (ra) yace Manzon Allah (saww) yace:
"KU NEMI TSARIN ALLAH DAGA RAMIN NAN NA BAKIN CIKI".
Sai suka ce "Ya Ma'aikin Allah shin menene Ramin Bakin ciki?".
Sai yace "WANI RAMI NE ACIKIN JAHANNAMA WANDA ITA JAHANNAMA TAKE NEMAN TSARIN ALLAH DAGA GARESHI KULLUM SAU DARI HUDU".
Sai suka ce "Ya Rasulallahi su waye zasu shiga cikinsa?".
Sai yace "AN TANADAR DASHI NE SABODA QURRA'U (MASU KARATU) WADANDA SUKE YIN RIYA DA AYYUKANSU. KUMA HAKIKA MALAMAN QUR'ANIN DA SUKE ZIYARTAR AZZALUMAN SARAKUNA, SUNA DAGA CIKIN WADANDA ALLAH YAFI QINSU DAGA CIKIN QURRA'U".
Ibnu Maajah da Tirmidhiy ne suka ruwaitoshi).
Acikin riwayar Sayyiduna Abdullahi bn Abbas (ra) Kuma, cewa yayi an tanadar da wannan ramin ne domin masu yin riya daga cikin al'ummar Annabi Muhammadu (saww).
Ya Allah ka kiyayemu daga wuta da azabar cikinta, Ka kiyayemu daga aikata duk wani abinda zai kusantamu gareta.
Ya Allah ka bamu aljannarka, Ka bamu yardarka, Ka sadamu da Annabinka (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam). Aaameeen.
DAGA ZAUREN FIQHU
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support