Masu hikima sunce ?? (fitowa ta 30) dr.mansur ibrahim sokoto ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Sunday 30 July 2017

Masu hikima sunce ?? (fitowa ta 30) dr.mansur ibrahim sokoto

MASU HIKIMA SUN CE

Fitowa ta 30

136. Idan ka zama mai girman kai mutane za su watse su bar ka

137. Idan Allah ya taimake ka ba mai kayar da kai. In ko ya kayar da kai to, ba mai tayar da kai.

138. Aikin da mutum ya yi da shi za'a yi masa sakayya. Iyakar manzoya fadi sako, a karba ko bada a karba.

139. Kada ka hana hannunka mika alheri, kada kuma ka yi ta mikawa har ka zama ba ka da ahin da za ka mika.

140. A duniya kowa ka gani yan aiki, to yana yi ne iya fahimtarsa. Duk wanda kake ganin sa a karkace shi a wurin sa daidai yake.


Littafin: Sheikh Baba Ahmad As-Shinkidi

Fitarwa da gyarawa: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

5/11/1438
29/7/2017

» Gabatarwa Zauren Minbarin Malamai +2347037477743
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support