Goron sallah daga (kitabu was-sunnah) ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 8 July 2017

Goron sallah daga (kitabu was-sunnah)

*GORON SALLAH???!!!*
.
.
*DAGA ZAUREN*
.
*KITABU WAS SUNNAH*
.
.
*ﻣﺠﻠﺲ ﺘﻌﻠﻴﻢ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ*
📓📔
Watsaps
08036222795
08136182627
:
Yau 13-10-1438, wacce tayi dai dai da 7-7-2017***
:
Itace ranarda cikin ikon Allah da amincewarsa muke fara gabatarda lekca me taken
.
*GORON SALLAH*
....
....
*ﺇﻥ ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ، ﻧﺤﻤﺪﻩ ﻭﻧﺴﺘﻌﻴﻨﻪ، ﻭﻧﺴﺘﻐﻔﺮﻩ، ﻭﻧﻌﻮﺫ ﺑﺎﻟﻠﻪ ﻣﻦ ﺷﺮﻭﺭ ﺃﻧﻔﺴﻨﺎ، ﻭﺳﻴﺌﺎﺕ ﺃﻋﻤﺎﻟﻨﺎ، ﻣﻦ ﻳﻬﺪﻩ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻼ ﻣﻀﻞ ﻟﻪ، ﻭﻣﻦ ﻳﻀﻠﻞ ﻓﻼ ﻫﺎﺩﻱ ﻟﻪ، ﻭﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺣﺪﻩ ﻻ ﺷﺮﻳﻚ ﻟﻪ ﻭﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻣﺤﻤﺪﺍ ﻋﺒﺪﻩ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ*
.
_Bayan haka Muna farawa da miqa dubban gaisuwa da dumbin salata marasa adadi, zuwaga uban dakinmu babban jagora Miji awajen zainab kuma baban Zainab, dan gatan Allah shugaban masu kyauta, kuma shugaban manzonni Annabinmu muhammad (s.a.w) Allah ta'ala yayi dadin tsira da daukaka a gareshi****_
                _Bayan haka 'yan uwan wannan wasu 'yan taqaitattun bayanaine muka qunsosu wayanda mukeso mu gabatar dasu gareku matsayin goron sallarmu gareku, dan kuwa yau kwanaki 13 kenan da muka kammala azumin watan ramadan wanda muke fata gamida roqon Allah madaukakin sarki yaji tausanmu ya kar6a mana wayannan ibadu da mukayi****_
              _Muna farawa da neman taimakon Allah madaukakin sarki da yabamu ikon rubuta abinda yake shine dai dai kuma yakauda alqalaminmu akan rubuta kuskure sannan kukuma masu karatu Allah ta'ala yabaku ikon fahimtar wannan bayanai namu a daidai kuma yabamu ikon amfanuwa da wayannan taqaitattun bayanai, dan kuwa zamuy qoqari matuqa wajen taqaitawa dan bamaso wannan lekca ta cika tsawo*****_
            _Amma wannan lekcar zamu dinga kawo wayansu ruwayoyine ta hanyar ishara wayansu kuma tahanyar rubuta fassarar larabcin batareda munkawo nassin bayanin da larabciba duk saboda qoqarnda mukeso muga munyi na taqaitawa*****_
            _Na'am abune wanda zanniya cewa baze yiwuba ace anyi magana akan Ruwan zam zam batareda an ambaci asalinsaba, To amma kasantuwar nafada cewa taqaitawa zamuyi, asali gameda ruwan zam zam yana farowane Lokacinda Annabin Allah Ibrahim yayi hijira daga mahaifarsa wato Qasar Iraqi bayan yasha gwagwarmawa da mahaifinsa da sauran jama'arsa akan suyi imani da Allah daya sesukaqi harma sukayi yunqurin jashe shi, wanda tsanani sadda yakai tsanani shine se Annabi Ibrahim ya dauki matarsa Saratu da Dan dan uwansu wato Annabi ludu yafita dasu akan zasuyi hijira****_
          _To a hanyar tasu sesuka biyo ta qasar masar wacce alokacin akwai wani azzalumin sarki wanda yake baza jakadunsa awannan gari suna tare baqi idan sukaga mutum yana tafe da mace kyakkyawa inhar aka bincika akaji cewa wannan mutuminda yake tareda wannan matar shine mijinta to wannan mugun sarkin ze qwace wannan matar yace shine ya cancanta yazama mijinta ba wannan ba****_
          _To Annabi Ibrahim kuma yasanda wannan batun yasan wannan aika aika ta wannan sarkin na masar mugu azzalumi***_
          _To lokacinda Annabi Ibrahim yashigo masar da matarsa sarah wacce a wannan lokacin ta manyanta wato dattijuwace amma kuma tsabar kyawunta yananan bai gusheba****_
         _Se Annabi Ibrahim yace mata idan aka tambayeki wanene ni?? Kice ni dan uwankine, nima kuma zance ke 'yar uwatace tunda kinga dai mune anan kawai musulmai dan haka ke 'yar uwatace a addini nima kuma dan uwankine a addini*****_
  _To shikuma wannan sarkin qa'idarsa itace in mace tace batada miji wannan da suke tare dan uwantane, to baze kar6etaba ze qyaleta, to awannan lokacinda wannan mamuguncin sarkin yaga tsabar kyawu na Sarah se kawai yakarya wannan qa'idar tasa, ya kar6e saratu a hannun Annabi Ibrahim (AS)******_



Ayi Haquri Zamu dakata anan sekuma bayani nagaba idan Allah yakaimu zamuji yadda takaya tsakanin Wannan Azzalumin sarki da wannan mata Sarah
:
:
_Almajirinku dan mutanen kabo_
'
_Jameel Alhassan HarunaY Kabo_
_Alwahhaby-Assalafy_
.
 Nake mana fatan Alheri wassalamu alaikum
..
.
.
Zaku iya samun shafinmu na facebook tawannan hanyar

http://m.facebook.com/Kitabu-Wassunah-1522000298067561/
.
ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪy ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.

Subhanak Allahumma wabi hamdika ash hadu anla ila ha illah anta astagfiruka  Wa,atubu ilaika
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support