WADANNE SHEKARUNE SUKE WAJIBI A KULA DASU YAYIN LAYYA? ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Monday 28 August 2017

WADANNE SHEKARUNE SUKE WAJIBI A KULA DASU YAYIN LAYYA?

*WADANNE SHEKARUNE SUKE WAJIBI A KULA DASU YAYIN LAYYA?*

الحمد لله، سبحانك اللهم لا علم لنا إلا ما علمتنا إنك أنت العليم الحكيم.

*AMSA:* Malamai sun hadu akan akwai wasu shekaru da shari'a ta iyakance wajan layya, bai halatta yin layya da dabbar data gaza daka suba.

Duk wanda ya yanka dabbar data gaza da shekarun layyarsa bata yiba.

An ruwaito hadisai dasuke nuni akan haka, Duba *Al-majmu'u na Nawawi*

*Bukhari ya ruwaito (5556) da muslim (1961)* daka bara'u bin Azib, yace wani dan'uwansa da'ake cewa abu burda ya tambayi manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, yayi layya da akuyar da bata cika shekara guda ba? Annabi yace: jeka kayi layya da ita,  Amma daka kai babu wanda ya halatta yayi da akuyar da batakai shekara daya ba,

*Musilm ya ruwaito hadisi (1963)* daka jabir Annabi Sallallahu Alaihi wasallam yace: ( kada ku yanka dabbar layya sai wacce ta cika shekara, saidai idan kunsamu kanku cikin qunci saiku yanka wacce bata kai shekaraba daka cikin tumaki,

Nawawi acikin Sharhin Muslim yace: Malamai Sukace: *"Musannah"* itace wacce ta tafi shekara ta biyu daka kowanne dangin dabbobin ni'ima *raqumi ko saniya, awaki da tumaki* zuwa sama, Wannan bayanine qarara akan bai halatta yanka wacce bata shekaraba inba Daka dangin tumaki ba, a kowanne hali.

*Alhafiz acikin Talkees (4/285)* yace: Zahirin hadisin ya nuna baya halatta yanka tunkiya ko rago wanda bai shekara ba, sai idan baka da halin siyan wanda yacika shekara ya tafi ta biyu, ijma'i abisa sabani, wajibine ayi tawilinsa, ya dauki abunda yafi falala, qaddarawarsa shine, Kada ku yanka dabba sai wacce ta cika shekara guda.

Haka Nawawi yace: acikin sharhin Muslim, da Aunul Ma'abuud.

Yazo acikin *Mausu'ah fiqhiyyah (5/83)* wajan Anbaton Sharadin layya.

Dabba ta kai shekarun layya, ta zama *"saniyyah"* raqumi ko saniya ko akuya *(jaz'ah)* ko wacce take sama da ita daka tumaki, bai halatta yin layya da dabbar da batakai *"saniyyah"* ba, Sai cikin tumaki, ko abunda bai kai *jaz'ah* cikin tumaki ba....

Wannan Sharadin An hadu akansa tsakanin malamai Saidai sunyi sabani akan fassarar *Saniyyah da Jaz'ah*.

Kamar yanda ibnu Abdul barri ya fada acikin *tarteebul Tamheed (10/267)*

Kamar yanda nawawi yace: acikin *Al-majmu'u (8/366).*

*Jaz'ah* a dangin tumaki, itace wacce ta cika wata shida awajan ```Hanafiyyah da Hanabila, a wajan Malikiyyah da shafi'iyyah itace: Wacce ta cika shekara.

Al-Musinnah: Daka akuyoyi itace: Wacce ta cika shekara daya,a wajan Malikiyyah da Hanafiyyah da Hanabila, Awajan shafi'iyya kua itace: wacce ta cika shekara biyu```

*Musinnah daka Shanu*: Itace wacce ta cika (shekara biyu) awajan *Hanafiyyah da Shafi'iyya da Hanabila*, Awajan malikiyyah itace: Wacce ta cika shekara uku.

*Musinnah cikin Raquma* itace: Wacce ta cika shekara biyar, awajan Hanafiyyah da Malikiyyah da Shafi'iyyaj da Hanabila.

Duba:- *Bada'i'il Sana'i'i (5/70) da Baharul ra'iq (8/202) da Attaaju wal-ikleel (4/363) da Sharhin Muktasarul khaleel (3/34) da Maj-mu'u (8/365) da Al-Mugny (13/368).*

Yazo afatawa lajnatul da'imah (11/377), Sukace:.

Dalilai na Shari'a Sun nuna ya halatta yin layya da, ( Tunkiya ko ragon da ya kai wata shida) akuya ko taure wacce ta cika shekara guda, Saniya ( Wacce ta cika shekara biyu) raqumi wanda ya cika (shekara biyar) Abunda yake qasa da Wadannan baya halatta ayi hadaya ko layya dashi, domin Dalilai na Qur'ani da Sunnah sahinsu yana fassara sashi.

Wallahu A'alamu.

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا أنت، أستغفرك وأتوب إليك.

*🖊Tambaya da Amsa Abisa fahimtar Magabata Na Kwarai*
*WhatsApp Group*
*2348123432272*

KARKU MANTA DA GAYYATO MANA ABOKANANKU ZUWA WANNAN SHAFIN MUN GODE.



Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support