Guzurin maniyyata aikin hajji ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Wednesday 2 August 2017

Guzurin maniyyata aikin hajji

*>>>GUZURIN MANIYYATA AIKIN HAJJI<<*


wallafar  *Mallam Abdus-salam Ibrahim Abubakar* Rahimahullahu

      GABATARWA

Da sunan Allah Mai Rahman Mai Jinqai, dukkan yabo da Godiya sun tabbata ga Allah wanda ya wajabta Aikin Hajji Akan Musulmai, tsira da amincin Allaah su tabbata ga manzon Allah SAW wanda yayi yayi Hajji yayi umara tsira da amincin Allaah su tabbata a gare shi da Alayensa da sahabbansa baki daya.

Bayan haka:-
Abinda yasa na rubuta wannan littafin shine saboda intaimakawa maniyyata zuwa aikin hajji musamman wayanda basa fahimtar rubutun larabci, saboda ganin kura kurai da wasu alhazai sukeyi yayin aikin hajjinsu, immadai saboda qarancin Ilimi ko kuma rashin fahimta. Ina Mai rokon Allah ya kar6i wannan aiki nawa kuma ya sanya shi a cikin mizanin ayyuka na na alkhairi kuma ya yafe kura kurai na da nayi a ciki. amin

Abdussalam Ibrahim Abubakar

wannan itace muqaddimar mallam kenan a lokacin rayuwarsa muna fata Allah ya jiqansa ya sanya wannan littafin sadaqatul jariya a gareshi mu kuma masu Rubutawa da karantawa Allah Yabamu ladan hakan yasa wannan littafin ya amfani mu duniya da lahira.


       *1 HAJJI*

hajji rukuni ne daga cikin rukunnan musulunci guda biyar. Kuma aikin hajji na wajibi sau daya ne a rayuwa, abinda ya qaru ya zama nafila.


*2 SHARUDDAN WAJIBAM HAJJI SUNE:-*

1.Musulunci
2.Balaga
3.Hankali
4.Yanci
5.Samun dama
Samun dama ya kasu kamar haka
@na dukiya ko guzuri,
&na lafiya ko qarfi.
6.Samum Dan rakiya ga mace.

*3 RUKUNNAN HAJJI*

¹ Yin harama
²Dawafin infada
³Sa'ayi tsakanin safa da marwa
⁴Tsayuwan Arfa

*4 WAJIBAN HAJJI*

¹ Yin harama a miqati
² Tsayuwan Arfa har rana ta fadi
³ Kwana a muzdalifa
⁴ Kwana a minna kwanaki biyu bayan Sallah
5 Yin Jifa
6 Aski ko saisaye
7 Dawafin bankwana ga wacca bata haila ko biqi.

*QARIN BAYANI (TANBIHI)*

Duk wanda yabar rukuni daga cikin rukunan hajji guda hudu to bashida hajji, harsai ya aikata shi. Wanda yabar wajibi daga wajiban hajji, hajjinsa yayi amma tilas sai yayi fidiya, Ya yanka dabba ya rabawa miskinai in bai samu ba sai yayi azumi kwana uku a can makka, Sannan yayi azumi Bakwai inya dawo garinsu, Ya zama goma kenan.

Anan zan dakata insha Allah gaba zan dora rubutu na 03 zamuyi bayani akan:-
ABUBUWA DA AKA HANA MAHAJJACI YINSU

Daga Dan uwanku *JAMEELU MASKA*


Majlisin sunnah facebook
www.facebook.com/majlisinsunnah

Majlisin Sunnah WhatsApp
+2348164363661

Instagram: muneerassalafy
E-mail: massalafy8@gmail.com
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support