_WANENE IBN TAIMIYYAH_(fitowa ta 5) ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Sunday 20 August 2017

_WANENE IBN TAIMIYYAH_(fitowa ta 5)

*_WANENE IBN TAIMIYYAH_*
➖➖➖➖5⃣➖➖➖➖
★ Ga masu bukatar page dinmu sai su shiga wannan link din suyi like  https://free.facebook.com/إبن-تيمية-رحمه-الله-136792630155923/?_rdr
.
_A rubutun mu daya gabata mukace Ko bayan komawarsa gida Shekhul Islam yaci gaba da samun matsaloli da malamai masu qaramin sani da taurin kai. Kamar yadda suka yi cah a kansa wai don yace, in mutum yayi rantsuwar saki kaffara kawai zai yi, aurensa na nan Haka ma don cewar da yayi saki uku na komawa daya idan anyi su a zama guda. Wadannan malamai basu samu sukuni ba sai da suka sa aka hana shi fatawa a shekarar 719H._
.
_A shekara ta 720H aka sake iza qeyar babban malamin zuwa gidan kaso in da ya share wata biyar da kwana goma sha takwas. A shekara ta 726H wasu alqalai sun tsoma bakinsu a cikin rikicin Ibnu Taimiyyah da maqiyansa, inda aka wallafa wata fatawa ta qarya aka jingina ta gareshi, wai ya haramta ziyarar qabarin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam dana sauran Annabawa, Alhalin shi kuwa ya rarrabe tsakanin ziyararsu ne ita kad'ai da kuma had'a ta da yin tafiyayya. Ya labarta sa6anin magabata a kanta, sannan ya nuna karkata ga hanawa idan ya kasance anyi tafiyayya saboda ita. Ya kuma bayyana hujjojinsa na ingantattun hadissai. Wannan rikicin ma dai sai da ya sake mayar da wannan bawan Allah a gidan maza, inda ya samu damar da ya yawaita wallafe- wallafe gami da bautar Allah Ta’ala A shekara ta 728H aka fitar da duk littafan da ke tare da shi da alqalumma da tawadar da aka samu a wurinsa, saboda wani malami da ake kira Ikhna’i ya kai qarar sa, don yayi masa raddi, kuma wai ya jahiltar dashi. A nan ya zama dole Ibnu Taimiyyah ya haqura ya duqufa ga zikiri da sallah da karatun Alqur’ani da yake wadannan suna a kansa tun zamanin quruciya._
.
_*RASUWAR IBN TAIMIYYAH* zamu cigaba in Allah ya yarda a darasi na gaba, ga Allah muke neman taimako_
.
*Hussaini Ibnu Taimiyyah Kuriga*
.
→ A yanzu haka zaku iya bibiyar zauren SA'ADATUL MUSLIM ta shafin sada zumunta dake Facebook ta cikin wannan link din
https://free.facebook.com/Saadatul-Muslim-Islamic-Group-Chat-1017855871594468/?ref=opera_speed_dial_freefb
.
→ Ga masu sha'awar shiga zauren SA'ADATUL MUSLIM sai su aiko da cikakken Suna da adreshi izuwa ga numbar mu +2348052975857 ta whatsapp


KARKU MANTA GAYYATO MANA ABOKANANKU ZUWA WANNAN SHAFIN MUN GODE.


Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support