Wai shin Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam) Umrah nawa ya yi kafin ya bar duniya? ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Friday 11 August 2017

Wai shin Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam) Umrah nawa ya yi kafin ya bar duniya?


​​​Assalamu alaikum
Wai shin Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam) Umrah nawa ya yi kafin ya bar duniya? Ba fa aikin hajji ba❌ no! Umrah​​​


​​AMSA:​​
*******

وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ


​An karbo Daga ​Qataadah​ cewa ​Anas (Radiyallahu Anhu)​ ya fada masa cewa ​Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam)​ yayi ​UMRAH​ ​SAU​ ​HUDU​ dukansu acikin watan Zhul Qi'dah banda Umrah da yayi tareda Hajjinsa:​
​(Yayi) Umrah daga Al-Hudaybiyah ko kuma a lokacin Al-Hudaybiyah acikin watan Zhul-Qi'dah, (ya sake yin) Umrah a shekarar data zagayo acikin watan Zhul-Qi'dah, kuma (yayi) Umrah daga Ja'raanah lokacin da ya raba ganimar yaqin Hunayn acikin watan Zhul-Qi'dah.​
​​(Bukhaari, Al-Hajj, 1654. Muslim, Al-Hajj, 1253).​​


​Ibn Al-Qayyim​ yace; ​(Manzon Allah) yayi Umrah sau hudu bayan hijrah,​ Umrah hudu dukansu acikin ​Zhul-Qi'dah.​
​Ta farko itace ​Umrah ta Al-hudaybiyyah​​ kuma itace ta farko acikinsu, a shekara ta 6 bayan hijrah, Amma mushrikai sun hanashi yakai ga daki ​(Ka'abah).​ Ya soke rakumansa na layyah a hudaybiyyah bayan an tare masa hanyar shiga Makkah, shi da sahabbansa sun aske gashin Kansu sannan sun fita harami, sun koma Madinah acikin wannan shekara.
​​Umrah ta biyu cikakkiyar Umrah ce​​ a shekara ta 7 bayan hijrah lokacin da ya shiga Makkah ya tsaya ciki har (kwana) 3 sannan ya fita bayan ya kammala Umrah.
​​Umrah ta uku​​ itace Umrah da yayi tareda ​Hajjinsa​
​​Ta hudu itace​​ Umrah daga ​Al-Ja'raanah,​ lokacin da ya fita yaqin ​Hunayn​ sannan ya dawo Makkah yayi Umrah daga Al-ja'raanah.

​IbnAl-Qayyim​ yace babu sabanin ra'ayin malamai akan cewa ​Umrah hudu ne yayi​
Duba:
​​(Za'ad al-Ma’aad, Mujalladi na 2, shafi na 90-93)​​


​Al-Nawawi yace:​
Malamai sunce: Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam) wadannan Umrah ne acikin waan Zhul-Qi'dah saboda ya nuna falalar watan Zhul-Qi'dah, ya kuma rusa ra'ayin zamanin jahiliyyah da suke tinanin yin Umrah cikin Zhul-Qi'dah yana cikin mafi munin mummunan aiki.

Saboda haka ​Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam)​ yayi Umrah har sau hudu acikin watan Zhul-Qi'dah saboda wannan itace gamsasshiyar hanyar nuna halaccin yin Umrah a watan Zhul-Qi'dah, da kuma nuna cewa tinanin jahiliyyah akan watan Zhul-Qi'dah karya ne.
​​(Sharh Muslim, 8/235)​​



والله أعلم،

***********************************


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.


​​🌙Tambayoyin​​ ​​Musulunci🌙​​
            ​​WhatsApp​​ ​​Group​​
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support