Guzurin maniyyata aikin hajji (fitowa ta 3) ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 5 August 2017

Guzurin maniyyata aikin hajji (fitowa ta 3)

​>>GUZURIN MANIYYATA AIKIN HAJJI<<<​

wallafar ​Mallam Abdus-salam Ibrahim Abubakar​ Rahimahullah

 Rubutu na uku 03


بسم الله الرحمن الرحيم

Mai Karatu in baka manta ba a rubutu na biyu mun dasa aya ne Akan bayanin Abubuwa da aka hana mahajjaci yinsu, yau kuma insha Allah zamuyi bayanin abubuwa da suke halal ne mahajjaci yayi su,

​ABUBUWA DA AKA HALASTAMA MAHAJJACI YINSU​

1.wanka da wanke kai ko tsefe kai koda gashin ya zuba babu laifi.

2.wanke tufafi wanda akayi harama dashi ko kuma a canza shi asa wani

3.Yin qaho ko tsaga

4.yanke qumba wacca ta karye.

5.cire dankwali ga mace ko kwance kitso

6.shan inuwa da abinda baya ta6a kai kamar lema ko tanti da makamancinsu.

7.Sanya takalmi ko huffi amma karya rufe idon sawu.

8.Sanya zobe da Daura agogo do tabarau na ido.

9.wanda bai samu gyauto ba to ya halatta yasa wando.

10.Ya halatta ga mace tasa ko wanne irin kaya dako wane irin launi kamar, riga ko wando ko hijabi fari ko baqi ko shudi da makamantansu.

12.Ya halatta ga mace ta saukarda dankwalinta ko hijabinta har ya rufe mata fuska idon tazo kusa da maza ajanabiyyai. (wayanda ba muharramanta ba)

Anan zamu dakata insha Allah a rubutu na hudu zamuyi bayani akan, ABUBUWA DA SUKA KEBANCI MATA KADAI. watau hukunce hukuncen aikin hajji wanda mata kawai suka shafa.


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا أنت أستغفرك وأتوب إليك.

Daga dan uwanku ​JAMEELU MASKA​

Majlisin sunnah facebook
www.facebook.com/majlisinsunnah

Majlisin Sunnah WhatsApp
+2348164363661

Instagram: muneerassalafy
E-mail: massalafy8@gmail.com
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support