SHIN YA HALLATA 'YAN'UWA SU HADU SUYI LAYYA? ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Friday 25 August 2017

SHIN YA HALLATA 'YAN'UWA SU HADU SUYI LAYYA?

*SHIN YA HALLATA 'YAN'UWA SU HADU SUYI LAYYA?*

الحمد لله، سبحانك اللهم لا علم لنا إلا ما علمتنا إنك أنت العليم الحكيم.

*AMSA:* Layya ta isarwa Mutum da Iyalan gidansa Saboda hadisin Abu ayyubal Ansari Wanda *Turmuzi ya Ruwaito (1505) da Ibnu Majah (3147).*

Yazo acikin tuh-fatul Ahawazy, Wannan hadisin nassine akan akuya daya ta isarwa mutum da iyalansa, koda suna da yawa, wannan shine gaskiya.

Ibnul Qayyeem acikin zhadul Ma'ad yace: yana daka cikin shiriyar Manzan Allah Sallallahu Alaihi wasallam akuya ko tunkiya daya ta Isarwa mutum da iyalan gidansa koda sunada yawa.

Shaukany acikin Nailur Audaar yace: Gaskiya shine akuya ko tunkiya daya ta isarwa mutum da iyalan gidansa, koda su darine ko sama da haka, kamar yanda sunnah ta hukuntar da hakan.

Kamar yanda yazo acikin Taaj wal-ikleel sharhin Muktasarul khaleel (4/364).

Ya Halatta kasanya dan'uwanka cikin wadanda kayanka layya amadadinsu, idan kuna zaune agida daya Abuncinku daya.

Amma Idan kowa da gidansa kuma kowa da garin da yake da zama, Bazaka shigar dashi cikin layyarka ba, saidai shima yayi tasa shi kadai.

Ya halatta kasanya danka cikin layyarka koda mawadacine matuqar yana zaune agidanka kana ciyar dashi.

Wallahu A'alamu.

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا أنت، أستغفرك وأتوب إليك.

*🖊Tambaya da Amsa Abisa fahimtar Magabata Na Kwarai*
*WhatsApp Group*
*2348123432272*


Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support