SHIN DOLENE SAI MUSULMI ZAI YANKA DABBAR LAYYA? ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Wednesday 30 August 2017

SHIN DOLENE SAI MUSULMI ZAI YANKA DABBAR LAYYA?

*SHIN DOLENE SAI MUSULMI ZAI YANKA DABBAR LAYYA?*

الحمد لله، سبحانك اللهم لا علم لنا إلا ما علمتنا إنك أنت العليم الحكيم.

*AMSA:* Sharadine a yanka layya da niyyar layyace za'ayi,  idan mutum ya yanka da niyyar yaci nama layyar batai ba.

Imamun Nawawi Rahimahullahu yace: Niyya sharadice ta Ingantuwar layya.

*Al-Maj-mu'u (8/380).*

Bai Halatta ka wakilta kirista kafiri wajan yanka layya ba, tare da cewa yankan kirista halal ne aci, saidai saboda yankan layya ibadace, bai halatta ka wakilta kirista ba.

Saboda kirista bashi daka cikin Masu wannan ibadar da neman kusancin Allah, domin kafirine, ba'a karbar ibadarsa, idan bata halatta akaran kansa ba, bai halatta yayiwa wani ba,

Amma Da Mutum zai wakilta kirista ya yanka masa layya dan yaci nama babu laifi.

*Sharhin Mumti'i na Shaiek Usaimeen (7/494).*

Wallahu A'alamu.

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا أنت، أستغفرك وأتوب إليك.

*🖊Tambaya da Amsa Abisa fahimtar Magabata Na Kwarai*
*WhatsApp Group*
*2348123432272*

Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support