SHIN DABBA DAYA TA ISARWA MUTUM DA IYALANSA? ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Monday 28 August 2017

SHIN DABBA DAYA TA ISARWA MUTUM DA IYALANSA?

*SHIN DABBA DAYA TA ISARWA MUTUM DA IYALANSA?*

الحمد لله، سبحانك اللهم لا علم لنا إلا ما علمتنا إنك أنت العليم الحكيم.

*AMSA:* Dabba guda daya ta isarwa mutum da iyalansa da wanda yaso  ya sanyashi daka cikin musulmi.

Saboda hadisin Aisha Allah yaqara mata yarda tace :an kawowa Annabi Sallallahu Alaihi wasallam rago mai qaho, sai yace da ita, bani wuqa, saita kawo masa wuqa, saiya karbi wuqar ya kwantar da ragon sai ya yankashi, sai yace: Da sunan Allah, ya Allah ka karbawa muhammad, da iyalan gidan muhammad, da Al'ummar muhammad, Sannan yai layya dashi.

*Muslim*.

Daka Abu Ayyubal Ansary Allah yaqara masa yarda yace: Mutum azamanin Annabi Sallallahu Alaihi wasallam yana yin layya da Akuya ga kansa da iyalansa, suci naman su ciyar.

*Ibnu Majah da Turmuzi, Albani ya Ingantashi acikin Sahihu turmuzi (1216).*

Idan mutum yayi layya da tunkiya ko akuya ga kansa da iyalan gidansa, ta isarwa duk wanda ya sanya acikin niyyar yankan layyar cikin iyalansa wanda yake raye da Wanda ya Mutu,

Idan bai niyyaci komai ba, ya gamesu koya kebance, duk wanda yake ahlinsane ya shiga, a al'ada ko a luggah.

A al'ada ahlin gida sune matayen mutum da 'ya'yansa da 'yan'uwansa.

A lugga kuma dukkan wani makusancinsa cikin zurriyarsa da zurriyar babansa da zurriyar kakansa, da zurriyar kakan babansa.

Akuya ko tunkiya bata isarwa mutum biyu su hadu su saya suyi layya, saboda rashin ruwaito hakan daka Alqur'ani da Sunnah.

Kamar yanda bai halatta mutum takwas su hadu akan raqumi ko saniya ba,

Amma ya halatta mutum bakwai su hadu akan raqumi ko Saniya.

Amma Tarayya wajan lada wannan ba'a iya kanceba.

Wallahu A'alamu.

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا أنت، أستغفرك وأتوب إليك.

*🖊Tambaya da Amsa Abisa fahimtar Magabata Na Kwarai*
*WhatsApp Group*
*2348123432272*

KARKU MANTA DA GAYYATO MANA ABOKANANKU ZUWA WANNAN SHAFIN MUN GODE.


Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support