bayani daga farko har karshe akan yadda ake sallar gawa!!! ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 12 August 2017

bayani daga farko har karshe akan yadda ake sallar gawa!!!


​​​Assalamu alaikum
Malam Don Allah ina so ka yi mana bayani akan sallar gawa  domin gaskiya mutane da yawa bamu san yadda ake yin sallar ba illa muna tsaye ne kawai har a gama, abin yanada muni sosai ba kadan ba.​​​



​​AMSA:​​
*******

وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ،


Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam) da Sahabbansa (radiyallahu anhum) sunyi bayanin yadda ake yin Sallar Gawa. Ana yinta ne babu ruku'u babu sujuda. Kuma ana yinta ne kamar haka:

​1.​ Zakayi kabbara ta farko kace ​​Allahu Akbar​​ sannan kace ​​A'uzhu billahi minasshaydanir rajiim​​ sannan kace ​​Bismillahir rahmanirrahiim​​ sannan ka karanta ​​Suratul Fatiha​​ sannan ka karanta ​​gajeruwar Surah ko wasu ayoyi.​​

​2.​ Sannan kayi kabbara ta biyu kace ​​Allahu Akbar​​ sannan kayiwa Annabi salati, irin Wanda akeyi bayan tahiya cikin sallah.

​3.​ Sannan kayi kabbara ta uku, kace ​​Allahu Akbar​​ sannan kayiwa mamaci addu'a, wannan itace addu'ar da aka karbo daga Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam) kuma itace tafi inganci:

​​​ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺍﻏﻔﺮ ﻟﺤﻴﻨﺎ ﻭﻣﻴﺘﻨﺎ ﻭﺷﺎﻫﺪﻧﺎ ﻭﻏﺎﺋﺒﻨﺎ ﻭﺻﻐﻴﺮﻧﺎ ﻭﻛﺒﻴﺮﻧﺎ ﻭﺫﻛﺮﻧﺎ ﻭﺃﻧﺜﺎﻧﺎ، ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻣﻦ ﺃﺣﻴﻴﺘﻪ ﻣﻨﺎ ﻓﺄﺣﻴﻪ ﻋﻠﻰ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﻭﻣﻦ ﺗﻮﻓﻴﺘﻪ ﻣﻨﺎ ﻓﺘﻮﻓﻪ ﻋﻠﻰ ﺍﻹﻳﻤﺎﻥ، ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺍﻏﻔﺮ ﻟﻪ ﻭﺍﺭﺣﻤﻪ، ﻭﻋﺎﻓﻪ ﻭﺍﻋﻒ ﻋﻨﻪ، ﻭﺃﻛﺮﻡ ﻧﺰﻟﻪ، ﻭﻭﺳﻊ ﻣﺪﺧﻠﻪ، ﻭﺍﻏﺴﻠﻪ ﺑﺎﻟﻤﺎﺀ ﻭﺍﻟﺜﻠﺞ ﻭﺍﻟﺒﺮﺩ، ﻭﻧﻘﻪ ﻣﻦ ﺍﻟﺨﻄﺎﻳﺎ ﻛﻤﺎ ﻳﻨﻘﻰ ﺍﻟﺜﻮﺏ ﺍﻷﺑﻴﺾ ﻣﻦ ﺍﻟﺪﻧﺲ، ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺃﺑﺪﻟﻪ ﺩﺍﺭﺍً ﺧﻴﺮﺍً ﻣﻦ ﺩﺍﺭﻩ ﻭﺃﻫﻼً ﺧﻴﺮﺍً ﻣﻦ ﺃﻫﻠﻪ، ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺃﺩﺧﻠﻪ ﺍﻟﺠﻨﺔ ﻭﺃﻋﺬﻩ ﻣﻦ ﻋﺬﺍﺏ ﺍﻟﻘﺒﺮ ﻭﻣﻦ ﻋﺬﺍﺏ ﺍﻟﻨﺎﺭ ﻭﺍﻓﺴﺢ ﻟﻪ ﻓﻲ ﻗﺒﺮﻩ ﻭﻧﻮﺭ ﻟﻪ ﻓﻴﻪ، ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻻ ﺗﺤﺮﻣﻨﺎ ﺃﺟﺮﻩ، ﻭﻻ ﺗﻀﻠﻨﺎ ﺑﻌﺪﻩ.​​​

   ​​“Allaahumma ighfir li hayyinã wa mayyitinã wa shaahidinã wa ghaa’ibinã wa sageerina wa kabeerinã wa zakarinã wa unthaanã.​​
   ​​Allaahumma man ahyaytahu minnã fa ahyihi alal-Islam wa man tawaffaytahu minnã fa tawiffahu alal-imaan.​​
   ​​Allaahumma ighfir lahu warhamhu wa aafihi wa a’fu anhu, wa akrim nuzulahu wa wassi’i madkhalahu wagsilhu bil-maa’i wal-salju wal-barad, wa naqqihi minal khaadaaya kamã yunaqqaal thawbal abyadu minal danas.​​
   ​​Allaahumma abdilhu daaran khayran min daarihi wa ahlan khayran min ahlihi.​​
   ​​Allaahumma adkhilhu al-jannah wa a’izhu min azaabal qabri wa min azaabin naar wa afsah lahu fi qabrihi wa nawwir lahu fihi.​​
   ​​Allaahumma laa tahrimna ajrahu wa laa tadillanaa ba’dahu."​​

Idan mutum yayi addu'a da wash kalmomi babu laifi a hakan. Kamar yace:

_​​​ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺇﻥ ﻛﺎﻥ ﻣﺤﺴﻨﺎً ﻓﺰﺩ ﻓﻲ ﺇﺣﺴﺎﻧﻪ، ﻭﺇﻥ ﻛﺎﻥ ﻣﺴﻴﺌﺎً ﻓﺘﺠﺎﻭﺯ ﻋﻦ ﺳﻴﺌﺎﺗﻪ، ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺍﻏﻔﺮ ﻟﻪ ﻭﺛﺒﺘﻪ ﺑﺎﻟﻘﻮﻝ ﺍﻟﺜﺎﺑﺖ.​​​_

​​“Allaahumma in kaana muhsinan fa zid fi ihsaanihi wa in kaana musee’an fa tajaawaz an sayi’aatihi.​​
​​Allaahumma ighfir lahu wa thabbit-hu bil-qawlil-thaabit."​​

​4.​ Sannan kayi kabbara ta hudu kace ​​Allahu Akbar​​ sai kayi shiru na dan lokaci kadan, sannan saika sallame a gefenka na dama kace ​​Assalamu alaikum wa rahmatullahi.​​

Wannan shine takaitaccen abinda ya tabbata a Sunnah na Sallar gawa.

​Kitaab Majmu'ul Fataawa wa Maqaalaat Mutanawwi'ah li samaahatal Shaykh Abd al-Azeez ibn Abd-Allaah ibn Baaz (rahimahullah) Mujalladi na 13, shafi na 14}​



والله أعلم،

***********************************


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.


​​🌙Tambayoyin​​ ​​Musulunci🌙​​
            ​​WhatsApp​​ ​​Group​​
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support