Sako zuwa ga marasa lafiya ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Friday 18 August 2017

Sako zuwa ga marasa lafiya

SAKO ZUWA GA MARAR LAFIYA


ابن تيمية رحمه الله;
Yana cewa;
*"Mafi yawa daga cikin marar lafiya suna samun waraka da lafiyane saboda adduarsu da rokon da suke awajan Allah ko su sami waraka ta hanyar Ruqya da ayoyin alqurani da addu'o'in da Manzon Allah ﷺ ya koyar da dogaran zuciyarsu da Allah da kyautata zatonsu zuwa ga Allah,ba dan maganin da suka sha ba"*
@الفتاوى ج ٢١ ص ٥٦٣
Sakon da yake nan shine;
"Ya kai marar da lafiya ko wanda yake jiyar marar lafiya ku kyautata zaton waraka tana wajan Allah ba shan magani ba kadai ba kwarewar lafiya ba kadai,ku yawaita yin addua idan maku da lafiya tare da neman waraka ta hanyar karatun alqurani da addu'o'in da Manzon Allah ya koya,ko sha magani a matsayin sababin samun sauki sannan ku dogara da sauki yana wajan Allah kadai".

ابن القيـّم رحمـه اللـه:
Yana cewa;
*"Ambaton Allah da karatun alqurani da addu'o'i da komawa zuwa ga Allah da dogaro ga Allah da kiyaye sallah,yana warakar da masu rashin lafiya da yawa kuma yana yaye damu ga mutane da yawa da yardar Allah"*
@مفتاح دارالسعادة ١ / ٢٥٠ 

ابن القيم رحمه الله: 
Yana cewa;
*"Babu wata chuta daga cikin chutukan zukata da chutukan jiki,face acikin alqur'ani akwai waraka ta wannan chuta ko hanyar samun warakarta"*
@زاد المعاد[٤/٣٥٢]

Wannan yana nuna mana mu yawaita karatun alqurani zamu sami raka na dukkan chutukan mu dana yan uwanmu.

محمد بن نصر المروزي:
Yana cewa;
*"Bamu san wani aikin Dha'a ba da Allah yake tunkude azaba da damuwa saboda shi kamar Sallah"*.

ابن الجَوْزِي رَحِمَهُ الله:
*"Yawan karanta alqur'ani yana aiki wajan warakar rashin lafiyar zuciya da jiki wanda zuma da sauran magani baya iya warkarwa da yardar Allah"*
@"التبصـرة" صـ (٧٩) 

ابن حجر رَحِمَهُ الله:
Yana cewa;
*"Allah ya sanyawa Masoyansa mafi ga dukkan abinda ya dora masu na jarabawa,kadai yana jinkirta samun warakarsu ne idan basu da lafiya dan ya daukaka matsayinsu da yawaita ladarsu mai yawa"*
@فتح الباري 6/483


أبو إسحاق الحربي رَحِمَهُ الله:

Yana cewa;
*"Bana kai kukana zuwa ga Mahaifiyata ko yar uwata ko matata ko wajan ya'yana ko mutum babu abinda zai kara maka sai damuwa ka kai kuka zuwa ga Allah shi kadai,a wajansa ne ake samun maganin dukkan damuwa"*

Mahaifina yayi jiya tsawon shekara goma sha biyar bai taba kai kukasa ba zuwa ga kowa ba sai Allah shi kadai.

Nima shekarana goma ina gani da ido daya dayan baya gani amma ban taba kai kukana ba zuwa ga kowa ba.
@طبقات الحنابلة (٨٧/١).


الشيخ عبد الرحمٰن السعدي رَحِمَهُ الله:
Yana cewa;
*"Addu'a takobice ta mai karfi da mai rauni,makamine na samun waraka daga dukkan bala'i,da Adduane Annabawan Allah da siddiqai suke samun cin nasara"*
@مجموع مؤلفاته(٧٣٦/٢٣)


*اللهم الشفاء والطهور والنور والرفعة لجميع مرضى المسلمين*
              *اللهم امين*



*سبحان الله وبحمده عدد خلقه ورضا نفسه وزنة عرشة ومداد كلماتة سبحان الله العظيم ..*

KARKU MANTA DA GAYYATO MANA ABOKONANKU ZUWA WANNAN SHAFIN MUN GODE.



Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support