MENENE HUKUNCIN WANDA BAYA IYA HALATAR YANKA LAYYARSA,? ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Wednesday 30 August 2017

MENENE HUKUNCIN WANDA BAYA IYA HALATAR YANKA LAYYARSA,?

*MENENE HUKUNCIN WANDA BAYA IYA HALATAR YANKA LAYYARSA,?*

الحمد لله سبحانك اللهم لا علم لنا إلا ما علمتنا إنك أنت العليم الحكيم.

*AMSA :* Abunda yafi shine mutum ya halarci yanka layyarsa da kansa, idan bazai iyaba, babu laifi wani yaje ya shaida masa yankan layyar tasa.

Domin Wakilci wajan halattar yanka layya ya halatta babu Sabani tsakanin Malamai,

Halartar yanka layya mustahabbine ba dole ba.

Ibnu Qudama yace: Idan ya yanka layyar da hannunsa haka shine yafi, domin Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya yanka layyarsa da hannunsa.

Idan Kuma ya wakilta wani ya halatta, saboda Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya Wakilta Aliyu ya qarasa yanka Masa hadayarsa, wannan Babu Sabani akansa, An so ya halarci yanka layyar sa.

*Al-Mugny (13/389-390)*

Ladan layya idan bayarwa kayi ayi maka, dukkan wanda ka Niyyata acikinta zai samu ladan, koda baka halarci yanka taba, saboda fadin Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ( Dukkan Ayyuka Saida Niyyah, kowanne mutum akwai Abunda ya niyyata.

Wallahu A'alamu

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا أنت، أستغفرك وأتوب إليك.

*🖊Tambaya da Amsa Abisa fahimtar Magabata Na Kwarai*
*WhatsApp Group*
*2348123432272*


Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support