WACCE DABBA CE TAFI FALALA WAJAN YIN LAYYA DA ITA? ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Wednesday 30 August 2017

WACCE DABBA CE TAFI FALALA WAJAN YIN LAYYA DA ITA?

*WACCE DABBA CE TAFI FALALA WAJAN YIN LAYYA DA ITA?*

الحمد لله سبحانك اللهم لا علم لنا إلا ما علمتنا إنك أنت العليم الحكيم.

*AMSA :* Dabbar datafi falala wajan layya Itace (Raqumi) Sannan (Saniya) Sannan (Tunkiya) Sannan Tarayyah wajan yanka (Saniya) haka Abu Hanifa da Shafi'i sukace.

Saboda fadin Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ( Wanda yaje masallacin juma'a da Wuri asa'ar farko, Kamar ya gabatar da Sadakar ( Raqumi ne) Wanda yaje asa'a ta biyu kamar ya gabatar da ( Saniya) ne, Wanda yaje a sa'a ta uku kamar ya gabatar da (da rago mai qaho ) ne, Wanda yaje a sa'a tahudu kamar ya gabatar da ( Kaza)ne, Wanda yaje Asa'a ta biyar kamar ya gabatar da ( Kwai) ne,

*Bukhari (881) da Muslim (850).*

Domin yankane da'ake neman kusancin Allah dashi, sai raquma tafi falala kamar hadaya, yi da Rago yafi falala akan mutane su hadu suyi da (Raqumi) domin Zubar jini shine manufa a layya, Wanda yake shi kadai zai samu kusancin Allah da zubar dashi baki daya, A cikin tumaki da awaki rago shine yafi falala, domin dashi Annabi Sallallahu Alaihu wasallam yayi layya, saboda yafi kyawun nama.

*Duba Al-Mugni (13/366).*

Kamar Yanda yazo a *fatawa Lajnah (11/398).*

Abunda ake hujja dashi cikin hadisin shine yanda aka samu fifikon kusantar Allah tsakanin (Raqumi da Saniya) da (Tumaki da Awaki) Saboda raqumi yafi kudi da yawa da nama da amfani, Haka Malaman mazhabobi ukun nan sukace: *Abu hanifa, da Shafi'i, da Ahmad*.

Imamu Malki yace: Abunda yafi falala wajan layya shine ragon daya shekara daya, sanann Saniya, sannan Raqumi.

Domin Annabi Sallallahu Alaihi wasallam yayi layya da raguna guda biyu, shi kuwa Annabi Sallallahu Alaihi wasallam baya aikata abu sai wanda yake yafi falala.

Amsa akan wannan sai ace: Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya zabi ragone don sauqaqawa Al'ummarsa, domin suna koyi dashi, Bayaso ya taqurawa Al'ummarsa, haqiqa Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya bayyana falalar raqumi akan Saniya.

Wallahu A'alamu.

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا أنت، أستغفرك وأتوب إليك.

*🖊Tambaya da Amsa Abisa fahimtar Magabata Na Kwarai*
*WhatsApp Group*
*2348123432272*



Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support