Hukuncin qasru 5 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Friday 7 July 2017

Hukuncin qasru 5

*HUKUNCIN SALLAR QASRU-5!!!???*
.
.
*DAGA ZAUREN*
.
*KITABU WAS SUNNAH*
.
.
*ﻣﺠﻠﺲ ﺍﻟﺘﻌﻠﻴﻢ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ*
📓📔
Watsaps
08036222795
08136182627
.
.
Taken Lekca........
.
*SALLAR QASRU!!!!??*
.
Wannan shine bayani na biyar****
.
Cigaba***
.
.
_Kwanakin baya nataba yin wani rubutu gameda sallar qasru, nace batada adadin kwanaki, toh hakika nasamu kalubale meyawan gaske musamman awajen masu taqlidanci da mazhabar malikiyya, sunci mutuncina sosai saboda nace sallar qasru batada adadin kwanaki, wanda hakan kuma su yasabama mazhabarda sukebi ta malikiyya, wacce nakawo muku fahimtar imamu malik acan baya inda nace dashi da Shafi,i da wasu malamai suna ganin cewa anayin qasrune kwanaki uku kawai, wato matafiyi idan yayi tafiya zeyi qasrune na kwanaki uku, inhar kawuce kwanaki uku acan garinda kaje sukace zaka cika sallah***_
.
_Toh Alhamdulillahi nidai ba dan malikiyya bane, sannan kuma ba imamu malik nakebiba, Annabi muhammad aka turomin ba imamu malik ba***_
.
_Amma aqidarda nakeba ta salaf, mu awajenmu kaunar Imamu malik Addinine, kuma aqidace, awajenmu duk wanda bayason imamu malik toh dan bidi,ane, kuma makiyinmune, saboda hadisanda muke aiki dasu, wayanda Imamu malik yaruwaito muna basu wata daraja ta musamman, amma munada tabbacin imamu malik yana kuskure tunda shima mutum ne kamar kowa kuma ba ma,asumi bane, sannan kuma akwai malamai dayawa wayanda suka fishi ilimi da daraja nesa ba kusaba, tunda shi imamu malik ba sahabi bane, baiga manzon Allah ba, sannan kuma ba tabi'i bane tunda bai taba gani wanda yaga manzon Allah ba, amma munyarda cewa babban malamine wanda zan iya cewa azamaninshi babu irinshi, kuma aqidarshi aqidace mekyau wanda muke kyautata masa zato, kuma muna sonshi fiyeda yadda mukeson iyayenmu wayanda suka haifemu***_
.
_Amma shi imamu malik da bakinshi yake cewa *MA MINNA ILLA RADDUN, WA MARDUDUN ALAIHI* wato dukkanmu malaman musulinci muna acikinmu kowannenmu yana yima wasu raddi, kuma shima ana yimai raddi, ashe kenan ba abun mamaki bane dan imamu malik yabada fatwa anki akarbeta wannan baya nuna cewa an wulakanta malik kokuma anzageshi***_
.
_Kukaranta Sweedy acikin tanwirul hawalik, yakawo maganar imamu malik lokacinda Sarki Abdulmalik yanemeshi da yabada muwaddarshi dan tazama kundin musulinci wacce za,arika hukunci da ita adukkan kasashen musulinci, amma imamu malik sai yace: Aa sahabbai sun watsu aduniya kuma sun watsa karatu dan haka akwai hadisai dayawa wayanda ni bansansuba dan haka baze yiwuba ace littafina kadai za,a rika hujjah dashi***toh kunji imamu malik dakanshi yayiwa ilimi Adalci toh danme wani ayau zezo yace dole semunbi mazhabar malikiyya??_
.
_Imamu malik watarana yatara dalubanshi yakaisu gaba qabarin manzon Allah, yace musu duk duniya babu wanda ba,a daukar maganarshi a ajje wacce bata daceba, face wanda yake cikin wannan qabarin, toh ashe kenan ba abin mamaki bane dan munce abar fahimtar imamu malik awajenda yayi kuskure shinema yace muyu hakan, kunga kenan munsawa hatta shi kanshi imamu malik idan muka bishi awajenda yayi kuskure***_
.
_mu awajenmu duk wanda ya rusa imamu malik toh yarushe 50% kashi hamsin cikin dari na hadisanda muke kafa hujjah dasu***_
.
_Kuma naji kuna korafi dan munce Sahihul bukhari shine mafi ingancin littafin hadisi, toh da kunnena naji wani malami dasunan da,awar sunnah wai yana kokarin kare imamu malik naji yanata cin mutuncin imamu shafi,i da imamul bukhari, harma yana cewa wai duk hadisanda suke cikin bukhari wai bolace na hadisanda imamu malik ya watsar wayanda basu ingantaba wai sune imamul bukhari yakwaso yazuba acikin littafinshi***_
.
_Toh wannan maganar karyace zunzurutu kuma son zuciyace kokuma jahilci, amma abinda shi wancan malamin besaniba shine: Na,am bama shakka cewa Imamu malik nesa ba kusaba yafi bukhari daraja, kuma yafi bukhari kota waccce fuska, toh amma abinda yafaru shine: bukhari besamu ganin imamu malik ba, toh amma kusan zan iya cewa kakaf daluban malik wayanda sukayi ruwayar muwadda awajenshi, dukansu saida bukhari yabisu daya bayan daya yakoyi hadisai awajensu kuma muwaddar suka koya mishi, wannan yasa zakaga hadisi abukahri kuma kaganshi acikin muwadda, wanda hakanma yana nuna karyar shi wancan malamin, tunda yace duk hadisanda suke cikin bukhari wayanda malik ya watsar ne, toh wannan karyane tunda ga hadisainan rututu a bukhari kuma sunanan jibge acikin muwadda***_
.
_kai kusanma ince maka babu wani hadisinda yake bukhari face yananan acikin muwadda, sedai kila kai muwaddarda take ahannunka yazama babu hadisib aciki, saboda mutane dayawa sun ruwaito muwadda awajen imamu malik, amma kuma inka hada muwaddodin zakaga ba hadisai iri daya bane acikinsu, zakaga wannan malamin yaruwaito hadisin wancan kuma bai ruwaitoba, toh bukhari duk wayanda sukai ruwayar muwadda awajen malik seda yabisu yakoyi muwadda awajensu***_
.
_misali Muhammad Ibn Hassan Ahs shaibani, wanda shinema yaba bukhari shawarar yadage yakoyi ilimin hadisi, saboda afarko bukhari ya shagaltune da koyon ilimin fiqhu***_
.
_kunga kenan saimuce bukhari Almajirin almajiran malik ne, kuma koda ake cewa sahihul bukhari yafi muwadda inganci, saboda bukhari tunfarko saida yayima kanshi sharadi cewa bazai kawo hadisinda bai ingantaba acikin wannan littafin nashi, sannan kuma cewa akayi bukhari yafi muwadda inganci, ai wannan ba suka bane ga imamu malik, darajacema muka kara mishi, tunda hadisanshine sukafibyawa acikin bukharin***_
.
_Ayi hakuri jama,a munsaki asalin karatun munkoma wata magana, toh itama wannan maganar tanada fa,idarta awannan lekcar saboda wata kurace muke dan takewa saboda korewa mutanenmu shubuharda ake dankara musu***_
.
_kuma ana cewa wai manhajin salaf damukace munabi, wai mazhabace ta Nasirudden Albani, toh wannan kuma karyace, tun kafin asan za,a haifi kakan kakan Albani malamai suke kira abi manhajin salaf, Kukaranta Imamus sabuni, wanda yau yafi shekara dubu da mutuwa musammab ya wallafa littafi yasamai suna *AQEEDATUS SALAF, ASHABUL HADIS****_
 .
_akoma a karanta muqaddimar Risala, ta Ibn Abu zaid Alqirawani cewa yake Abi manhajin salaf, sannan kuma can karshen risala wasiyyarda yakara yi kenan cewa arike manhajin salaf, wanda duniya tayi shaida akan cewa mai risala dan malikiyyane, harma cemai ake *IMAMU MAKIK KARAMI* toh tayaya wani dan son zuciya ayau zerika zagin malamai yana cewa sune suka kawo cewa abi manhajin salaf***_
.
_Kukaranta dan podio acikin littafanshi irin Nasihatu Ahliz zaman dasu Ihya'us sunnah dasauransu shima cewa yake lallai abi manhajin salaf***_
.
_idan akace salaf ana nufin malamai wayanda suka rayu a shekaru 300 na farkon musulonci, wayannan sune salaf, wanda imamu malik yana cikinsu, toh sunefa ake cewa ayi watsida duk wata fahimta ta wani malami azo arike tasu, duk wanda yazo a bayan shekaru 300 na farkon musulinci ba,a kiranshi salaf sedai idan yayi koyi dasu sai akirashi salafy, kuma Allah shine yafara kira da abi manhajin salaf***_
 .
_karanta suratul baqara ayata 137 Allah yace: *IDAN KUKAYI IMANI DA IRIN ABINDA WAYANCAN MAGABATAN SUKAYI TOH KUN SHIRYU, INKUWA KUKA JUYA MUSU BAYA TOH KUNFADA CIKIN HALLAKA* wannan ayar qur,anice jama,a kuje kuduba fassararta***_
.
_barema Imamu malik har yamutu besanda wata mazhaba malikiyyaba, kuma betaba cewa abi malikiyyaba, kai cewa yayi: *BABU ABINDA ZAI GYARA WANNAN AL,UMAR FACE ABINDA YA GYARA WAYANDA SUKA GABACETA* toh da wacce hujjah zakuce mubar abinda yake shine daidai muzo dole dole mubi mazhabar malikiyya???**_
 .
_kukaranta Ibn Abdulbarri akan fatwar imamu malik dayace adadin gejin kwanakin jinin haihuwa kwanaki 60 ne, Ibn Abdulbarri yace wannan fatwar imamu malik ce, amma mu mazhabar malikiyya fatwarmu shine jinin haihuwa baya wuce kwanaki 40, kunji shima ya ajje fatwar imamu malik yadauki hadisin Annabi toh danme kukuma zakuce mu mu ajje hadisi mudauki fatwar imamu malik???***_
.
_Kuyi hakuri kubiyoni cikin bayani nagaba semu koma kan asalin karatunda mukeyi***_
.
.
_Almajirinku kamar kullun_
.
```Jameel Alhassan Haruna Kabo```
_(Abu khausar)_
 .
.
.
.
Zaku iya samun shafinmu na facebook tawannan hanyar
https:/t/m.facebook.com/Kitabu-Wassunah-1522000298067561/
.
ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.

Subhanak Allahumma wabi hamdika nash hadu anla ila ha illah anta nastagfiruka  Wanatubu ilaika
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support