*```Assalamu alaikum*```
*```Tambaya na shine:*```
*```Idan mutum ya rasu ya bar Mata guda daya1 da 'ya'ya maza guda uku 3 da 'ya mace guda daya1, kuma ya bar dukiya ta miliyan takwas da dubu 'dari biyar (8.5million). Ya Kason kowa zai kasance?*```
_*AMSA:*_
*******
وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ،
Abu Na farko daza'a aiwatar akan dukiyar mamaci shine biyan bashi da wasiyya, kafin a shiga gundumar rabon gado.
Idan namiji ya rasu yabar mata daya da yara maza uku (3) da 'ya mace daya.
Idan wadannan sune magadansa kadai wadanda ya bari.
To anan kason matar zai kasance 1/8 (Sumuni) Na dukiyar da yabari, 'yarsa daya mace za'a bata Rabin kason namiji daya.
Kamar yadda Allah ya fada acikin Suratun Nisaa'i ayah ta 11 da 12.
ﻳُﻮﺻِﻴﻜُﻢُ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻓِﻲ ﺃَﻭْﻟَﺎﺩِﻛُﻢْ ۖ ﻟِﻠﺬَّﻛَﺮِ ﻣِﺜْﻞُ ﺣَﻆِّ ﺍﻟْﺄُﻧْﺜَﻴَﻴْﻦ
Allah yana yimuku wasiyyah acikin 'ya'yanku, namiji yanada rabon mata biyu.........(Nisaa'i 11)
ﻭَﻟَﻬُﻦَّ ﺍﻟﺮُّﺑُﻊُ ﻣِﻤَّﺎ ﺗَﺮَﻛْﺘُﻢْ ﺇِﻥْ ﻟَﻢْ ﻳَﻜُﻦْ ﻟَﻜُﻢْ ﻭَﻟَﺪٌ ﻓَﺈِﻥْ ﻛَﺎﻥَ ﻟَﻜُﻢْ ﻭَﻟَﺪٌ ﻓَﻠَﻬُﻦَّ ﺍﻟﺜُّﻤُﻦُ ﻣِﻤَّﺎ ﺗَﺮَﻛْﺘُﻢْ ﻣِﻦْ ﺑَﻌْﺪِ ﻭَﺻِﻴَّﺔٍ ﺗُﻮﺻُﻮﻥَ ﺑِﻬَﺎ ﺃَﻭْ ﺩَﻳْﻦ
........Kuma (Su Matan) sunada rubu'i daga abinda kuka bari (Na dukiya) idan reshe ('ya'ya) bai kasance ba gareku, to, idan kuwa reshe ya kasance gareku, to sunada sumuni (1/8) daga abinda kuka bari, daga bayan wasiyya wanda kukayi ko kuma bashi (debt)............(Nisaa'i 12).
Reshe acikin ayah ta 12 yana nufin 'ya'ya. Idan miji ya mutu yabar mata ita kadai babu 'ya'ya, to rabon ta shine 1/4.
Idan kuma akwai 'ya'ya to rabonta shine 1/8 kamar yadda ya tabbata a ayar.
A tambayar mu ta sama. Namiji ya rasu yabar masu gadonsa kamar haka:
1. Mata daya
2. Yara Maza uku (3)
3. Yarinya daya
Sannan yabar kudi naira miliyan takwas da dubu dari biyar:
N8,500,000
Ga yadda kason kowa zai kasance:
MATA
******
Za'a bata 1/8 Na N8,500,000
Shine ya kama miliyan daya da dubu sittin da biyu da naira dari biyar.
====N1062500
Idan an cire rabon matarsa, za'a bar N7,437,500.
Anan maza uku ne, kowanne kashi biyu za'a bashi, mace kuma kashi daya.
Idan ka hada kashi biyu sau uku zai baka kashi shida.
(2×3)=6
Sannan a tara da kashi daya Na mace zai bamu kashi bakwai
6+1=7
Yanzu zamu raba N7,437,500 zuwa gida bakwai
(N7,437,500/7)==N1062500.
Mace kashi daya
Kowanne namiji kashi biyu.
Kashi biyu zai bamu
1062500+1062500
==N2,125,000
YARA MAZA
**************
Kowannensu zai samu " Naira Miliyan biyu da dubu dari da ashirin da biyar"
======N2,125,000
'YARSA MACE
***************
Zata samu "Naira miliyan daya da dubu sittin da biyu da naira dari biyar"
======N1,062,500.
والله أعلم،
***********************************
سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.
_*🌙Tambayoyin*_ _*Musulunci🌙*_
_*WhatsApp*_ _*Group*_
_*+2347068043652*_
_*+2348164884055*_
*```Tambaya na shine:*```
*```Idan mutum ya rasu ya bar Mata guda daya1 da 'ya'ya maza guda uku 3 da 'ya mace guda daya1, kuma ya bar dukiya ta miliyan takwas da dubu 'dari biyar (8.5million). Ya Kason kowa zai kasance?*```
_*AMSA:*_
*******
وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ،
Abu Na farko daza'a aiwatar akan dukiyar mamaci shine biyan bashi da wasiyya, kafin a shiga gundumar rabon gado.
Idan namiji ya rasu yabar mata daya da yara maza uku (3) da 'ya mace daya.
Idan wadannan sune magadansa kadai wadanda ya bari.
To anan kason matar zai kasance 1/8 (Sumuni) Na dukiyar da yabari, 'yarsa daya mace za'a bata Rabin kason namiji daya.
Kamar yadda Allah ya fada acikin Suratun Nisaa'i ayah ta 11 da 12.
ﻳُﻮﺻِﻴﻜُﻢُ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻓِﻲ ﺃَﻭْﻟَﺎﺩِﻛُﻢْ ۖ ﻟِﻠﺬَّﻛَﺮِ ﻣِﺜْﻞُ ﺣَﻆِّ ﺍﻟْﺄُﻧْﺜَﻴَﻴْﻦ
Allah yana yimuku wasiyyah acikin 'ya'yanku, namiji yanada rabon mata biyu.........(Nisaa'i 11)
ﻭَﻟَﻬُﻦَّ ﺍﻟﺮُّﺑُﻊُ ﻣِﻤَّﺎ ﺗَﺮَﻛْﺘُﻢْ ﺇِﻥْ ﻟَﻢْ ﻳَﻜُﻦْ ﻟَﻜُﻢْ ﻭَﻟَﺪٌ ﻓَﺈِﻥْ ﻛَﺎﻥَ ﻟَﻜُﻢْ ﻭَﻟَﺪٌ ﻓَﻠَﻬُﻦَّ ﺍﻟﺜُّﻤُﻦُ ﻣِﻤَّﺎ ﺗَﺮَﻛْﺘُﻢْ ﻣِﻦْ ﺑَﻌْﺪِ ﻭَﺻِﻴَّﺔٍ ﺗُﻮﺻُﻮﻥَ ﺑِﻬَﺎ ﺃَﻭْ ﺩَﻳْﻦ
........Kuma (Su Matan) sunada rubu'i daga abinda kuka bari (Na dukiya) idan reshe ('ya'ya) bai kasance ba gareku, to, idan kuwa reshe ya kasance gareku, to sunada sumuni (1/8) daga abinda kuka bari, daga bayan wasiyya wanda kukayi ko kuma bashi (debt)............(Nisaa'i 12).
Reshe acikin ayah ta 12 yana nufin 'ya'ya. Idan miji ya mutu yabar mata ita kadai babu 'ya'ya, to rabon ta shine 1/4.
Idan kuma akwai 'ya'ya to rabonta shine 1/8 kamar yadda ya tabbata a ayar.
A tambayar mu ta sama. Namiji ya rasu yabar masu gadonsa kamar haka:
1. Mata daya
2. Yara Maza uku (3)
3. Yarinya daya
Sannan yabar kudi naira miliyan takwas da dubu dari biyar:
N8,500,000
Ga yadda kason kowa zai kasance:
MATA
******
Za'a bata 1/8 Na N8,500,000
Shine ya kama miliyan daya da dubu sittin da biyu da naira dari biyar.
====N1062500
Idan an cire rabon matarsa, za'a bar N7,437,500.
Anan maza uku ne, kowanne kashi biyu za'a bashi, mace kuma kashi daya.
Idan ka hada kashi biyu sau uku zai baka kashi shida.
(2×3)=6
Sannan a tara da kashi daya Na mace zai bamu kashi bakwai
6+1=7
Yanzu zamu raba N7,437,500 zuwa gida bakwai
(N7,437,500/7)==N1062500.
Mace kashi daya
Kowanne namiji kashi biyu.
Kashi biyu zai bamu
1062500+1062500
==N2,125,000
YARA MAZA
**************
Kowannensu zai samu " Naira Miliyan biyu da dubu dari da ashirin da biyar"
======N2,125,000
'YARSA MACE
***************
Zata samu "Naira miliyan daya da dubu sittin da biyu da naira dari biyar"
======N1,062,500.
والله أعلم،
***********************************
سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.
_*🌙Tambayoyin*_ _*Musulunci🌙*_
_*WhatsApp*_ _*Group*_
_*+2347068043652*_
_*+2348164884055*_
0 comments:
Post a Comment