Kissar Annabi Adam (AS) “No-1” ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 14 October 2017

Kissar Annabi Adam (AS) “No-1”

Kissar Annabi Adam (as) Na Farko
(1)
KISSAR ANNABI ADAM NA FARKO (AS)
Shida Annabi Adam (As) an halicce shine daga abubuwa guda 2 wato jiki da ruhi,kuma shine jiki na faro da All.. Madaukakin sarki ya taba halitta ,kana aka hura masa rai aka rayar dashi ya zama ya samu kamala ta halittar sa ayoyi daban daban acikin Al’kur’ani sunyi maganganu masu yawa game da aka halicci Annabi Adama (As) wanda hakan ke kara tabbatar da lallai an halicci Annabi Adam ne daga Turbaya, All.. Madausarkiya fadi acikin Alkur’ani cewa lallai All.. ya zabi Annabi Adamu da Nuhu da Ali Ibarahim akan dukkan talaikai, don haka lokacin da All.. yayi nufin halittar Khalifansa wanda zai zama shugaba mai shiryarwa a bayan kasa sai ya bijiro da wannan labarin ga Mala’iku amma sai malak’iku sukaji mamakin wannan labari, sai suka koma ga kawukan su suna magana cewa Ashe All.. zai halicci wata halitta da zai sa ta kasance khalifar sa a bayan kasa wadda zai yi wahala ya kasance mai ilimice da tsarki da tusayi kammar saruan halittun ubangiji dake sama, domin kafin halittar Adam All.. ya halicci wasu mutane wadanda suka tafka zamba da fasadi a bayan kasa , don haka sai suka cewa ubangiji ashe zaka sanya wadanda zasuyi barna da fasadi su zubda jini a bayan kasa? alhali mu muna tsarkake ka muna tasbihi gareka, amma saboda da hikimar da yasa All.. Madaukakin sarki ya halicci Annabi Adam da yake ilimi ne na gaibu babu wanda ya sani banda ubagiji sai All. Ya basu amsa da cewa hakika nasan abinda baku sani ba game da halittar Annabi Adam, don haka nema bayan da All.. Madaukakin Sarki ya Halicci Annabi Adamu (As) sai ya sanar da shi sunayen abubuwa yadda zai iya amfana dasu a bayan kasa ba tare da yasha wahala ba, daga nan sai All.. ya umarci su da suyi sujuda gareshi kuma su girmama shi domin yana dauke da ilimin da su basu dashi, kuma irin kallon da sukeyi masa na kaskantarwa su dawo daga rakiyar sa, wannan yasa ma aka bijirowa da mala’iku sunayen wasu abubuwa kuma akace su fadi sunayen su amma sai suka kasa bada Amsa amma da aka bijiro dasu ga Annabi Adam sai ya fadi sunayen su daya bayan daya, daga nan ne All.. madaukakin Sarki yace musu ashe bance muku nasan abinda ku baku sani ba, sai sukace ya ubangiji mu ba muna nuna rashin amincewar mu da nufin ka ba ne, To a nan ne batun kamalar dan Adam zai zo Inda All.. Madaukakin Sarki ya bukaci ya Annabi Adam zuwa wata kamala ta kololuwa inda anan ne All.. Madaukakin Sarki ya umarci mala’iku da suyi sujuda ga Annabi Adam (As) dukkansu sai sukayi Sujuda banda Iblis shine kawai yaki yin Sujuda yayi girman kai ya Kafircewa Ubangiji, sai dai All.. ya san dalilan da yasa bai yi Sujuda ga Annabi Adam ba, saboda yana ganin yafi Annabi Adama daraja domin shi an halicce shi ne daga lakka yayin da shi kuma Shedan an halicce shi ne daga wuta don haka ba zai yiyu wuta tayi Sujuda ga lakka ba, daga nan sai All. Madaukakin sarki ya koreshi daga Aljannah kuma ya la’ance shi ya zama tsinanne har zuwa ranar tashin Alkiyama sai dai shedan ya nemi All.. Madaukakin Sarki yayi Masar Rangwame ya kyaleshi har zuwa ranar tashin kiyama yace yayi Alkawarin sai yaa halakar da dukkan yayan Adam sai da wanda All.. ya kare daga cikin su, All. Madaukakin sarki ya fitar dashi daga Aljanna kuma yayi Al’kawarin sanya shi a cikin wuta da dukkan wadanda suka bi shi baki daya to bayan da aka fitar da shedan daga Al’jannah sai All. Madaukakin Sarki ya umarci Annabi Adamu da Hauwa’u da su shiga cikin aljanna su zauna domin su ji dadi daga ni’amar da All.. ya tanada acikin Aljnah, aka hallata musu dukkan abinda ke ciki amma sai aka hanesu daga cin wata bishiya, ko ma zuwa kusa da ita, kamar yadda yazo a cikin Alkur’ani mai girma cewa lokacin da aka cewa Annabi Adamu da Matar sa ku shiga cikin Aljanna kuma kuji daga dadin da aka tanadar muku aciki, kuma kada ku kusancin wannan bishiyar har dai zuwa karshen aya, amma sai shedan ya biyo su domin ya yaudare su ya halakar dasu kamar yadda yayi Alkawari, kuma ya sanya musu wasuwasi domin ya cire musu Surturar tsoron All. Da aka sanya musu na karama da kamala, , sai yace musu ubangjin ku ya hana ku cin wannan itaciyar ne ba don komai ba sai idan ku kaci wannan bishiyar to zaku zama mala’iku ne , ko kuma ku dawwama a cikin Aljannah, ya rantse musu cewa lallai ni ina son ku da Alkhairi ne, haka dai shedan yayi ta zawarcin su har ya kai ya yaudare su yasa suka ci wannan Itaciyar lokacin da haka ta faru sai suturar kamala da karama da aka sanya musu ta kwabe daga jikin su, anan All. Maduakakin sarki yayi magana da Annabi Adam (AS) cewa ashe ban hana ku cin wannan bishiyar ba, kuma ban gaya muku cewa shedan makiyin ku bane? Nana da nan sai Annabi Adamu da Hauwa’u suka gane kusakuren da sukayi amma nan ba yana nufin sun yi laifi bane kamar yadda sauran mutane sukeyi ba ne a’a sun bar abinda ake kira da tarkkir Aula ne wato barin abinda ya yafi dacewa amma ba laifi bane domin su Annabawa basa zunubi basa laifi, wanan kenan to daga nan sai suka nemi gafarar ubangiji game da barin abinda ya dace da sukayi, sai All. Ya fitar da su daga cikin Aljannah ya saukar dasu a gidan duniya kamar yadda yazo a cikin Alkur’ani mai girma ” sai shedan ya yaudaresu ya fitar dasu daga inda suke wato aljannah ke nan sai akace ku sauka cikin duniya sashin ku yana adawa da sashi kuma za’a sanya ku tabbata a kasa ku ci gaba da rayuwa har zuwa karshen rayuwar ku, kuma duk wanda ya bi shiryarwar ubangiji kuma bai aikata wani zunubi ba a bayan kasa to mummunar makoma ba zata shafe shi ba. Ya zo acikin tarihi cewa dukkan abubuwa dake cikin Aljannah All.. Madaukakin Sarki ya halartawa Annabi Adam da matar sa banda itaciya daya da aka hanashi ya kusance ta, to shin wacce irin bishiya ce ? Marigayi Allama Dabrasi ya bayyana a cikin Littafin Tafsirin sa na Majma’ul Bayan cewa yazo a cikin ruwayoyi wannan itaciyar Itaciya ce ta Alkama wato kafin ta girma ta isa yankewa, wata ruwayar kuma ta nuna cewa itaciyar Inabi ce kafin ta rika, sai dai Allama Dabrasi ya kara da cewa baya ga batun bishiyar Al’kama da Inabi ruwayoyin da aka samu daga Imam Ali (As) sun nuna cewa wannan Itaciyar itacen Kafur ne,
ku Kasance Tare Damu A Wani Post Na Gaba Kan Ci Gana Da Karatu.

Source: www.sunnahmedia.com.ng

SHIGA NAN DOMIN JOINING FACEBOOK GROUP DINMU

https://m.facebook.com/groups/129667237690008?ref=bookmarks
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support