Hukuncin sallar qasru 2 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Thursday 6 July 2017

Hukuncin sallar qasru 2

*HUKUNCIN SALLAR QASRU-2!!!???*
.
.
*DAGA ZAUREN*
.
*KITABU WAS SUNNAH*
.
.
*ﻣﺠﻠﺲ ﺍﻟﺘﻌﻠﻴﻢ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ*
📓📔
Watsaps
08036222795
08136182627
.
.
Taken Lekca........
.
*SALLAR QASRU!!!!??*
.
Wannan shine bayani na biyu****
.
Cigaba***
.
_Imamul Qurduby yace: Toh wancan hadisinda mukaji na ya,ala shima wasu daga cikin daluban Shafi,i sun kafa hujjah dashi cewa  yana kara tabbatar mana da halascin ayi sallar qasru koda ba,a halin tsoroba, kenan yazama sabanin waccan fahimtar tasu Malam Abubakar Gummi dasauran magabata wayanda sukace ba,ayin qasru sai ana halin tsoro, toh ga hadisi karara manzon Allah yace ita qasru sadakace garemu, dan haka yace mukarbi sadakar Allah***_
.
_sannan qurdubi yakara da cewa: ai ita sallar tsoro ba,a lurada wayancan sharuddan acikinta, (sharuddan sune farkon Ayar Allah yace: Babu laifi agareku idan kunyi tafiya, toh cewa idan kunyi tafiya wannan sharadine, saikuma inda yace: inkunajin tsoron kafirai zasu fituneku, toh shima wannan sharadine, kenan ba,ayin qasrun sallah se anceka wayannan sharadda idan muka duba zahirin ayar kenan) toh shine qurdubi yake cewa aima ita sallar tsoro sam ba,a duba wayannan sharuddan idan za,ayita, saboda ai koda bamuyi tafiya abayan kasa ba, se kawai kafirai suka biyomu garinmu misali zasu yakemu acikin garinmu ai yahalasta muyi sallar tsoro, bazamu tsaya kokarin cika sharuddanba***_
.
_Wannan magana ta qurdubi itama tana kara nuna mana cewa eh lallai ya halasta muyi qasrun sallah ahalin tafiya koda tafiyar bata yaki bane kuma ba,a halin tsoroba***_
.
_misali kaine zakaje kauyenku ziyara, kokuma zakaje kasuwanci ko aikin hajji misali duk kaga wannan tafiyar aidai babu tsoro, toh amma yahalasta kayi qasrun sallah, shine mafi ingancin magana kuma shine yadace da wancan hadisin na ya,ala***_
..
.
_Malamai sun sake tafka wani sabani akan shin waima sallar qasru dolene kokuwa ba dole bace???_
.
_nasan baku ganeba, toh ina nufin idan kayi tafiya kai amatsayinka na matafiyi, shin wajibine akanka dole sai kayi qasrun sallah kokuwa ba dole bane?? Toh shine nace malamai sunyi sabani gameda hakan***_
.
_Ansamu ruwayoyi daga manyan malamai dayawa wayanda suke ganin cewa yin qasrun sallah ga matafiyi dole ne, wannan shine Zancen Umar Ibn Abdul,azeez, da mafi yawan malaman kufah, wato iraqi kenan ayau, kuma wannan shine fahimtar Isma'il Alqadi, da  Hammadu bin sulaiman, kuma sun kafa hujjah da hadisin Aisha (Ra) tace: Afarkon musulinci Anfarlanta sallah raka bibbiyu ahalin zaman gida dakuma halin tafiya, amma daga baya, bayan isra,i da mi,iraji kenan, sai aka kara tsawon sallar gida takoma raka,a hudu, amma aka tabbatarda sallar matafiyi a raka,a bibbiyun,...****_
.
_Toh amma wasu malamai sukace babu wata hujjah acikin wannan hadisin saboda ita kanta Aisha ta kasance tana cika sallah ahalin tafiya***_
.
_Imamul Qurdubi acikin tafsirinsa yakawo wata fatwar imamu malik inda shima yake bayan wayanda suke ganin lallai dolene matafiyi yayi sallar qasru, inda imamu malik yace: duk wanda yacika sallah ahalin tafiya toh zesake wannan sallar matukar lokacinta bai fitaba***_
.
_Imamu shafi,i kuwa cewa yayi, nidai banaso inga mutum yana cika sallah ahalin tafiya saboda kwadayin dacewa da sunnah***_
.
_Sekuma musake komawa kan wancan hadisin na Ya,ala bin umayya wanda Annabi (s.a.w) yace: Ita qasru sadakace wacce Allah yayima bayi......***Toh wasu malamai sun kafa hujjah da wannan hadisin wajen cewa lallai yin qasrun sallah ahalin tafiya ba dole bane, saboda Annabi (s.a.w) cewa yayi sadaka ce, sukace ai ita sadaka yinta da karbanta ba dole bane, idan da manzon Allah yana nufin dolene da baze kirata sadaka ba sedai yace mata zakka***_
..
_Toh sekuma wayancan malaman wayanda suke ganin lallai yin qasru dolene, suma se suka sake daukar shi wannan hadisi, suka aunashi da wata qa,ida ta usul, inda malaman usul suke cewa: *AL AMRUL YAQTADIL WUJUB* wato umarni yana hukunta wajabci: sesukace toh ai acan karshen hadisin Annabi (s.a.w) yace; kukarbi sadakar ubangijinku, toh cewarda Annabi yayi kukarba, sukace ai wannan shima umarnine dan haka lallai yahukunta cewa dolene matafiyi yayi sallar qasru ba wai zabi bane ake bashi***_
.
_Toh amma atakaice dai, kada mutsawaita harshe akan wannan kadiyyar ita kadai toh bari mu takaita, lallai mafi ingancin magana shine yin qasrun sallah ga matafiyi ba dole bane, saboda Allah cewa yayi babu laifi akanku kuyi qasrun sallah***_
.
_Atakaice dai yin qasrun ba dole bane, ammadai wanda yayi qasru yanada falala fiyeda wanda yacika sallah, saboda dacewarda yayi da sunnah***_
.
_kenan semuce yin qasrun shine yafi akan acika, ammadai ba dole bane***_
.
_Ma,anar dole kuma a sallar qasru shine: bayan kayi tafiya kafara qasru na wani dan lokaci, toh bakada ikon cewa ka fasa yin ita qasrun, awajen malamanda suke ganinta amatsayin dole****_
.
.
_zan dakata anan sefitowa tagaba zamuji wasu muhimman bayanan_
.
.
.
_Almajirinku kamar kullun_
.
```Jameel Alhassan Haruna Kabo```
_(Abu khausar)_
 .
.
.
.
Zaku iya samun shafinmu na facebook tawannan hanyar
https:/t/m.facebook.com/Kitabu-Wassunah-1522000298067561/
.
ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.

Subhanak Allahumma wabi hamdika nash hadu anla ila ha illah anta nastagfiruka  Wanatubu ilaika
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support