Wanda ya wanke gawa mai zaiyi shin dolene shima sai yayi wanka?? ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Thursday 12 October 2017

Wanda ya wanke gawa mai zaiyi shin dolene shima sai yayi wanka??

*WANDA YA WANKE GAWA MAI ZAIYI SHIN DOLENE SHIMA SAI YAYI WANKA?*

الحمد لله.

AMSA: Abunda yake ingnatacce daka cikin magan-ganun malamai shine wanda yaiwa gawa wanka, wanka ba wajibine akansaba mustahabbine sunnah ne anso yayi in baiyi ba bashida laifi, ba dole bane.

Shine maganar *Abdullahi dan Abbas da Abdullahi dan Umar, da Aisha, da Hasanul Basari da Ibrahimun-naka'iy, da Shafi'i da Ahmad, da Ishaq, da Abussauri, da Ibnu munzir damasu ra'ayi irinnasu, ibnu qudama yarinjaar da hakan*.

Duba *Sunanu Turmizi ( 3/18) da Al-mugni ( 1/134)*

Shaik Albani Allah yajikansa yace: Mustahabbine gawanda yawanke gawa shima yayi wanka saboda fadin Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam, ( Wanda yawanke mamaci yai wanka, wanda yadauki mamaci yayi alwala) Abu dauda yafitar dashi *( 2/62-63) da turmuzi ( 2/132 )* kuma wasu hanyoyi na hadisin kyawawane wasu kuma ingantattune abisa sharadin da imamu muslim yake ruwaito hadisi, ibnul qayyem ya koro hanyoyin hadisin acikin *Tahzeebul Sunan* guda goma shadaya sannan yace: wadannan hanyoyin suna nuna lallai hadisin kiyayyene an haddaceshi.

 Albani yace:
Ibnu qaddan ya ingatashi hakama ibnu hazam acikin *Al-muhallah ( 1/250- (2/23-25,) da Alhafiz ibnu hajar acikin Attalkees ( 2/134) yace: Mafi saukin halin hadisin ace kyakkyawane*

zahirin Umarnin yana nuna wajabci, bazamuce wajibi bane saboda hadisai guda biyu wanda sukeda hukuncin hadisi marfu'i.

Nafarko: Shine fadin Abdullahi dan Abbas Allah yakara yarda dasu yace: ( Babu wanka akanku idan kun wanke mamaci, domin matacce acikinku ba najasa bane, yawadatar inkun wanke mamacinku kuwanke hannayenku)

*Hakim yaruwaitoshi ( 1/386) da Baihaqy ( 3/389)*

Sannan daka baya dalilai suka bayyana agareni hadisin mauqufine, bayan natabbar darauninsa abaya acikin sil-sila za'ifah ( 6304).

Nabiyu: fadin Abdullahi Dan Umar Allah yakara musu yarda yace: ( Munkasance muna wanke mamatanmu daka cikinmu akwai wanda yake alwala akwai wanda yake wanka)

Dabarani ya ruwaitoshi *(191) da khadibul bag-dadi acikin tarihinsa ( 5/424) da isnadi ingantacce kamar yanda hafiz yace: imamu Ahmad yai ishara akan hakan, Hakika khadeeb yaruwaito cewa yakebance dansa da rubuta wannan hadisinne, duba Ahkamul jana'iz ( 71-72).*

shine Abunda majalisar malamai dafatawa nakasar saudiyya suka rinjyar *( 1/318) da shaik Usaimeen Allah yajikansa, acikin sharhin mumti'i ( 1/295)*

Dan haka wanda ya wanke gawa  alwala ko wanka zaiyi, suma sunnah ne badole bane inya wanke hannunsama kawai babu komai akansa.

Amma wanke kaya ko riga bashida asali acikin shari'ar musulunci bidi'ane, Wallahu A'alamu.

سبحانك اللهم وبحمدك نشهد أن لا إله إلا أنت نستغفرك ونتوب إليك.

🖊 *Tambaya da Amsa Abisa fahimtar magabata Nakwarai*
*WhatsApp Group*
*+2348123432272.*
*+2348140925493.*


Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support