ANGO YA MUTU KAFIN AMARYA TA TARE, YAYA BATUN GADO DA TAKABA ? Dr.jamilu yusuf zarewa ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Monday 23 October 2017

ANGO YA MUTU KAFIN AMARYA TA TARE, YAYA BATUN GADO DA TAKABA ? Dr.jamilu yusuf zarewa

*_ANGO YA MUTU KAFIN AMARYA TA TARE, YAYA BATUN GADO DA TAKABA ?_*


*_Tambaya_*


Assalam Alaikum, Dr. an daura auren wasu yau ba'a dauko amarya ba sai gobe, amma Allah yayi wa angon rasuwa..tambayata anan wai shin za tayi takaba? Kuma tanada gadonshi?


*_Amsa_*
Wa'alaykumussalam

To dan'uwa idan miji ya mutu bayan an daura aure kafin ya tare da amryarsa, ya wajaba amaryarsa ta yi masa takaba, kuma a bata gadonta cikakke, kamar yadda Annabi S.a.w. ya yi hukunci da hakan ga Barwa'u 'yar Washik lokacin da mijinta ya mutu kafin su tare a hadisi mai lamba ta: 1145, wanda Tirmizi ya rawaito kuma ya inganta shi .

Allah ne mafi sani.

*_Dr. Jamilu Yusuf Zarewa_*

1/05/2016

Ga dukkan mai son shiga *ZAUREN FIQHUS SUNNAH* sai ya yi saving wannan number +2348122248585  sannan ya tura da sunansa da adireshinsa ta whatApp. Duk abun da mutum ya turo matukar ba suna ba ne ba za a kula shi ba.
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support