HUKUNCIN AURE CIKIN AURE?? Dr.jamilu yusuf zarewa ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Monday 23 October 2017

HUKUNCIN AURE CIKIN AURE?? Dr.jamilu yusuf zarewa

*HUKUNCIN AURE CIKIN AURE*


*Tambaya*

Assalamu alaikum, mallam tambaya muke da ita. Mace ce aka aurar
tana ‘yar-shekara 14 ga wanda bata so, to sai
mijin yayi tafiya har tsawon wata hudu (4) To
sai matar tasa aka rubuta mata saki tace ya
saketa, bayan ya dawo yace bai saketa ba,
amma ba’a yarda ba.
Da ta kare idda tayi aure
da wani har suka haihu, daga baya kuma suka
rabu, kuma yanzu ta ga musifu suna ta
samunta, sai take tunanin ko wancan abin ne da
tayi. Tana neman fatawa, ina hukuncin ta, da
yaran data haifa da miji na biyu?


*Amsa*
Wa'alaykumussalam

Malam amsar wannan tamba yana da mutukar
wahala, saidai na nemi taimakon wasu daga
cikin malamaina, ga abin da na samo :

1. Abin da ta yi mummuna ne a shari’ar
musulunci saboda ta yi aure cikin aure.

2. Zaman da su ka yi da mijinta na biyu, a
matsayin mazinaciya take, saboda haka duk
kwanciyar da suka yi da wannan mijin na ta
zina ne.

3. Yaran da su ka Haifa da mijnta na biyu,
‘ya’yansa ne, tun da bai san abin da ya faru ba
a baya.

4. Har yanzu igiyar aurenta ba ta warware ba
tsakaninta da mijinta na farko, saboda haka har
yanzu ita matarsa ce saidai in ya sake ta.

5. Mijinta na farko, zai iya dawowa da ita, ba
tare da sake daura aure ba, saidai dole sai
bayan ta tuba, domin ita a matsayin
mazinaciyya take, kuma Allah ya hana auren
mazinaciya.

6. Ya wajaba a gare ta ta yawaita istigfari
saboda girman zunubin da ta aikata.

7. Zai yi kyau su je wajan Alkali wanda ya san

shari’ar musulunci, domin ya yi musu hukunci.

ALLAH NE MAFI SANI.

*Dr. Jamilu Zarewa*

20/11/2016
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support