RIGIJI GABJI! Ina Malikawan Nigeria! Toh yau dai ga Imamu Malik yayi gabas Dr Ahmad Gumi yayi kudu. ! ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Thursday 19 October 2017

RIGIJI GABJI! Ina Malikawan Nigeria! Toh yau dai ga Imamu Malik yayi gabas Dr Ahmad Gumi yayi kudu. !

DAGA MIMBARIN SALAFIYYAH NETWORK NIGERIA
!
LALLAI INDA MALIKIYYAR SUKE YI DA GASKE TOH DA KASHE DR AHMAD GUMI KAWAI ZA AYI DOGARO DA FATAWAR IMAMU MALIK DANGANE DA DUK WANDA YAYI MUSUN CEWA QUR'ANI BA MAGANAR ALLAH BANE INDAI HAR BAI TUBA YA JANYE KALMAR BA.
!
RIGIJI GABJI! Ina Malikawan Nigeria! Toh yau dai ga Imamu Malik yayi gabas Dr Ahmad Gumi yayi kudu.
!
Wannan ke 'kara tabbatar da cewa An shigo cikin rigar malikiyya ne kawai ana ta fesa ma al'umma gubar mu'utazilanci a Masallacin Sultan Bello Kaduna. Allah (T) ya ce AlQur'ani maganarshi ce Dr Ahmad Gumi kuma ya ce A'a halittar Allah ne. Lallai inda ace malikiyyan da ake yi na gaskiya ne toh da kashe Dr Ahmad Gumi kawai ya kamata ayi dogaro da wannan bayanin na Imamu Malik acikin wannan rubutun kamar haka:

قيدة الإمام مالك )رحمه الله( في القرآنذكر الإمام البخاري في )خلق أفعال العباد( عن مالك قوله"القرآن كلام الله"وذكر اللالكائي بسنده عن أبي محمد يحيى بن خلف المقري قال كنت عند مالك بن أنس سنة ثمان وستين فأتاه رجل فقال يا أبا عبد الله ما تقول فيمن يقول القرآن مخلوق قال "كافر زنديق اقتلوه"وذكر اللالكائي أيضا عن أبي الحسن بن العطار محمد بن محمد قال سمعت شريح بن النعمان يقول سالت عبد الله بن نافع وقلت له إن قبلنا من يقول القرآن مخلوق فاستعظم ذلك ولم يزل موجعا حزينا يسترجع قال عبد الله بن نافع قال مالك بن أنس من قال القرآن مخلوق يحبس حتى يعلم منه توبةوذكر ابن أبي حاتم بسنده عن ميمون بن يحيى البكري قال قال مالك بن أنس من قال القرآن مخلوق يستتاب فإن تاب وإلا ضربت عنقهوجاء في المدونة "قال ابن نمير: سمعت أبا مصعب يقول: سمعت مالكاً يقول: القرآن كلام الله غير مخلوق، قال أبو مصعب فمن شك أو وقف فهو كافر".وفي ترتيب المدارك للقاضي عياض" "قال ابن أبي أويس سمعت مالكا يقول: )القرآن كلام الله وكلام الله منه وليس من الله شيء مخلوق(
!
Fassara:
Imamul Bukhaariy ya ambaci maganar Maaliku cewa " Alƙur'aani maganar Allaah ne" (Khalƙu Af'aalil Ibaad)Kuma Allaalikaa'iy ma ya ambata daga Baban Muhammad Yahya ɗan Khalaf Almuƙ'riy yace: ina wajen Maaliku ɗan Anas a shekara ta ɗari da sittin da takwas,yayin da wani mutumi ya ce: Allaah gafarta baban Abdullaahi (Imamu Maalik) me zaka faɗi game da wanda yake cewa Alƙur'aani HALITTA ne? Sai yace:"KAAFIRINEZINDIƘI, KU KASHESHI"
!
Har ilaa yau Allaalikaa'iy ya saake ambata daga baban Alhasan ɗan Al-Atɗaar Muhammad ɗan Muhammad yace naji Shuraihu ɗan Annu'umaan yanacewa na tambayi Abdullaahi ɗan Naafi'u na ce dashi ansami daga cikin mutananmuwanda yake cewa ALƘUR'AANI HALITTA NE! sai hankalinshi ya tashi dajin haka, kuma bai gushe ba yana mai takaicin maganar da nuna damuwa matuƙa yana istirjaa'i (salati), Abdullaahi ɗan Naafi'u sai yace Maaliku ɗan Anas yace:DUK WANDA YACE ALƘUR'AANI HALITTANE za'a tsare shi har sai an tabbatar ya tuba daga shi (wannan muguwar aƙidar).
!
Ɗan Baban Haatimu ya ambaci magana ta hanyar Maimuun ɗan Yahaya al-Bakariy cewa Maaliku ɗan Anas yace: DUK WANDA YACE ALƘUR'AANI HALITTA NE, ZA'A NEMESHI DA YA TUBA, INYA TUBA SHIKENAN, IN KUWA YAƘI ASARE WUYANSA.Yazo a cikin Mudawwana (littafin Maalikiyyah) cewa " ɗan Numairin yace: naji baban Mus'abu yana cewa: naji Maaliku yana cewa: ALƘUR'AANI MAGANAR ALLAAH NE ba halitta bane.Sai baban Mus'abu yace: Duk wanda ya yishakkar haka ko kuma yace shi baruwanshi (ba zai ce halittane ko ba halitta ba) KAAFIRINE.
___________________
Muhammad Shittu Abu Uwaisat.
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support