Dr. Gumi ya ce SALAF basu yi magana ba akan cewa shin Alqu'ani maganar Allah ne ko halittar sa ne ?? TOH AMMA KO SHIN WANNAN MAGANAR NA BABAN BOLA GASKIYA NE? ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Thursday 19 October 2017

Dr. Gumi ya ce SALAF basu yi magana ba akan cewa shin Alqu'ani maganar Allah ne ko halittar sa ne ?? TOH AMMA KO SHIN WANNAN MAGANAR NA BABAN BOLA GASKIYA NE?

AN ZO INDA SU SHEIKH SA'IDU MAI KWANO GUSAU DA SHEIKH ALBANIY ZARIA SUKA CE MANA ANA NAN BABAN BOLA ZAI ISO WURIN.
!
BABAN BOLA YA JEFO WASU BOMABOMAN AMMA MALLAM  ABU AHMAD ATEEQ SULAIMAN YA TARWATSA SU DA IZININ ALLAH ASA'ILIN DA YA KAI ZIYARA BABBAN SHAFIN DA YAKE JAGORANTA NA 'YAN 'KUNGIYAR ANTI HADITH.
!
Dr. Gumi ya ce SALAF basu yi magana ba akan cewa shin Alqu'ani maganar Allah ne ko halittar sa ne ?? TOH AMMA KO SHIN WANNAN MAGANAR NA BABAN BOLA GASKIYA NE??
....
AMSA:
Mallam Abu Ahmad Ateeq yace: Dr. Gumi 'karya yake yiwa SALAF _ kuma dama ya saba yi musu 'karya _ , wannan mas'alar tana daga cikin matsalolin da babu wani littafi na SALAF da zaka ga bai tattauna ta ba . Da ace Dr. Gumi ya karanta littafin RISALA na fi'khun MALIKIYYAH , da yaga yanda SALAF suka tattauna mas'alar tun daga mu'kaddimar littafin .

2. Dr. Gumi yace malaman Musulmi magabata sun yi kuskure saboda rashin sani , da suka tafi akan cewa AL'KUR'ANI MAGANAR ALLAH NE !!! TOH AMMA KO SHIN WANNAN MAGANAR NA BABAN BOLA GASKIYA NE??
..
AMSA :
Anan DR.GUMI ya warware maganar sa ta farko , ya fa'da cikin wacce tafi ta farkon muni !! Dama haka 'yan bidi'a suke , basa tabbatuwa akan matsaya 'daya ; kullun suna cikin ru'dani !!!
Bai kamata ba Dr. Gumi ya kuskurantar da magabatan Musulmi akan IJMA'IN su akan cewa Al'KUR'ANI MAGANAR ALLAH ne , tunda sun dogara ne akan nassoshi na shari'a akan wannan matsayar tasu , daga cikin nassoshin akwai kamar haka :
ALLAH YA CE :
" ﻭ ﺇﻥ ﺃﺣﺪ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﺸﺮﻛﻴﻦ ﺍﺳﺘﺠﺎﺭﻙ ﻓﺄﺟﺮﻩ ﺣﺘﻰ ﻳﺴﻤﻊ ﻛﻼﻡ ﺍﻟﻠﻪ "
Saboda haka , abunda ya kamata Dr. Gumi yace shine
:
" Allah ya yi kuskure da yace Al'ku'ani maganar sa ne
...
3. Dr. Gumi yace SALAF da suka ce Al'kur'ani maganar Allah ne , hakan da suka ce babu komai lura da yanayin zamanin su , amma Mu a wannan zamanin dolene mu sauka dàga wannan matsaya ta SALAF , sai mu 'kudurta cewa Al'kur'ani HALITTA ne !! TOH AMMA KO SHIN WANNAN MAGANAR NA BABAN BOLA GASKIYA NE??
..
AMSA :
A'a Dr. Gumi , Mu SALAF sun wadatar damu , kuma Mu bama ganin AQIDAR MUSULUNCI tana sauyawa saboda banbancin zamani . Amma kai da kake ganin ana iya yiwa musulunci
gyare _gyare sa'banin yanda yake , to kana iya fita ma daga cikin sa , wannan matsalar ka ce !!!
!
MU TARA A DARASI NA GABA DON JIN CI GABAN WADANNAN AQEEDUN MU'UTAZILAWAN DA AKE DASAWA A MASALLACIN SULTAN BELLO KADUNA.  ALLAH (T) MUKE ROKO DA YA TSARE MANA IMANINMU.
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support