Abubuwan guda 4 suna amfanar mutum bayan mutuwarsa. ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Sunday 8 October 2017

Abubuwan guda 4 suna amfanar mutum bayan mutuwarsa.

ABUBUWAN GUDA 4 SUNA AMFANAR MUTUM BAYAN MUTUWARSA



*1-Yi Masu addu'a dayi masu Istighfari da nema masu gafara da afuwa a wajan Allah yin hakan yana da amfani mai yawa ga wadanda suka rasu*

Kamar yadda Annabi s.a.w ya fada;
*(Lallai mutum akan daukaka daraja mutum a aljanna,sai yace:daga ina wannan matsayin,sai ace dashi,daga Istighfari da yayanka sukeyi maka).*
@رواه ابن ماجة رقم 3660 وهو في صحيح الجامع 1617


*2-Yi masa Sadaka*
Saboda hadisin Nana A'isha R.A tana cewa *"Wani mutum ya fada ga Annabi s.a.w yace:Ya Annabin Allah,Mahaifiyata ta rasu an kasheta,kuma ina zaton da Allah ya bata damar magana da tayi Sadaka da wani abu daga cikin dukiyarta,Shin tana da Lada idan nayi mata sadaka yanzu??"* sai yace
*(Eh kayi mata sadaka)*

Daga Ibn Abas R.A yana cewa:
*"Lallai Sa'ad bn Ubbadah Mahaifiyarsa ta rasu lokacin bayanan,sai yace Ya Manzon Allah s.a.w,mahaifiyata ta rasu lokacin ni bananan,shin zai amfaneta ta sami lada idan nayi mata sadaka??"*Sai Manzon Allah s.a.w yace:
*(Eh kayi mata Sadaka)*sai yace to kazama Shaidha na bayar da sadakar Gonar Makhraf sadaka gareta"
@رواه البخاري:2756
Awata riwayar daga Sa'ad bn Ubbadah R.A yana cewa:
*"Nace ya Manzon Allah,Mahaifiyata ta rasu,shin idan nayi mata sadaka hakan zai amfaneta??"*
Sai yace*(EH)*sai nace wata Sadakace tafi girman matsayi da lada?? Sai yace:
*(Shayar da ruwa)*
@️رواه النسائي:3664

*3-Yi masa aikin hajji ko umara*

Yana daga cikin aiyukan alkhairi da suke amfanar mutum bayan mutuwarsa,yi masa aikin hajji da umara amma da sharadin wanda zaiyi masu aikin hajjin ko umara ya kasance sauke aikin hajjin nasa sannan yayiwa mamacin nasa.

Wata mata tazo wajan Manzon Allah s.a.w,sai tace ni nayi sadakar wata Kuyabga ga mahaifiyata da ta rasu.sai yace:
*(kin samin ladar hakan kuma an mayar maki da ita a matsayin gado)*sai tace Ya Manzon Allah ana binta bashin azumi wata daya,shin ko zan iya biya mata azumin?? Sai yace:
*(Eh ki rama mata wannan azumin)*sai tace;Bata taba yin aikin hajjiba ko sau daya ba,shin ko zan iya yi mata aikin hajji?? Sai yace:
*(Eh kiyi mata aikin hajji)*
@️رواه مسلم في صحيحه رقم 1149

*4-Cikasa alkwalinsa wanda bana sabon Allah ba*

Yana cikin abubuwan da akeyiwa mamace bayan rasuwar ya amfanesa,cika alkawalinsa ko bakancensa.saboda hadisin Ibn Abas R.A yana cewa:
*"Wata mata tazo wajan Manzon Allah s.a.w,sai tace;Lallai Mahaifiyata tayi bakancen yin aikin hajji,amma ta rasu bata cikasa bakancenta ba,shin zanyi mata aikin hajjin ne???*
Sai yace:
*(Eh ki cikasa bakancen aikin hajjinta,ki bani labarin da ana binta bashine shi zaki biya mata??)* sai tace:Eh sai yace:
*(To biyan bashin Allah shi yafi chanchanta biyasa)*
@البخاري


*Allah yayi Rahama da gafara ga dukkan musulman da suka rigamu gidan gaskiya*

        RUBUTAWA ✍

Sheikh Aliyu Muhammad  Said
         GAMAWA



Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support