Yadda Aka Bayyana Rahmar Tausayin Allah (SWT) A Kur'ani Sheikh Kabiru Haruna Gombe ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Friday 13 October 2017

Yadda Aka Bayyana Rahmar Tausayin Allah (SWT) A Kur'ani Sheikh Kabiru Haruna Gombe


Kamar yadda aka bayyana a cikin ayah ta sama ,Allah (swt) ya umarci bayin sa (su tausaya wa juna )saboda su sami rahmar sa, tare da shiga aljannah da samun saukin wajen  hisabi. Bayin Allah (swt)da suka sadaukar da rayuwar su wajen neman yardar Allah(swt), su kanyi kokari wajen bin umarnin Allah(swt). Kyakkyawar Imanin su da Allah(swt) yasa suka fahimci muhimmancin Tausayi da Rahma,kuma suna da yakinin cewa ba abinda zai faru sai da sanin Allah. Kuma sun gane muhimmancin tausayi da Rahmar ubangiji da yayi masu.kamar yadda aka sani masu imani suna da tunani da  natsuwa,sanin haka yasa  suka zama wayayyu a cikin al’umma,kuma suka tabbata masu  tausayi a cikin jama’ar musulmi.

 Marar mutunci ba zai tausayawa kowa ba,saboda baya tunanin kowa sai kansa,  kuma yana bada muhimmanci ne kawai akan abinda zai amfane shi da son zuciyar sa,shiyasa baya damuwa da halin kunci da wasu jama’ar musulmi suke ciki,bugu da kari ba su tausaya yan uwansu a duk hallin da suke ciki na damuwa.

Dalilin da yasa Bayin Allah(swt) suke sadaukar da kansu wajen taimako da tausayin juna saboda bin umurni Allah (swt).Kamar yadda  aka bayyana a cikin   Ayoyi masu yawa.’’ Allah ne mafi tausayin masu tausayi".Saboda wannan dalili bayin Allah (swt)masu Imani suke daurewa akan duk halin da suka samu kansu a ciki na kunci ko jin dadi.

Kamar yadda Allah ya saukar a cikin Alkur’ani maigirma , "Kuma ba domin falalar Allah ba a kanku da rahamar sa … Kuma lalle ne Allah Mai tausayi ne,Mai jinkai)." (Surat an-Nur: 20). Aya ta sama tana nuna yadda  Allah yake tausaya wa bayinsa ,kuma yadda yake umurtar su dasu tausaya wa junansu,ta haka  suma zasu samu yardar Allah(swt) da tausayin sa.Shiyasa masu Imani suka dauki matsayin tausayi da  muhimmanci,kuma suna fatan samun rahmar Allah(swt),kuma suna tausaya wa al’umma,suna kokarin wajen umurtar al’umma dasu tausaya wa juna domin ta haka ne za’a samu rahmar Allah (SWT).

Gaskiya  Alkur’ani maigirma  yayi bayani akan dukkan al’amari da ya shafi tausayi da yadda za’a tausaya wa juna .Matsayin bayin Allah nagari sune masu tausaya wa da tabbatar da adalci a lokacin daya dace cikin al’umma kamar yadda Allah (swt)yayi umurni.
Kamar yadda aka bayyana  tausayi a Alkur’ani maigirma,Tausayi yana da babban matsayi da girman gaske  fiye da dukkan sauran al’amura.Jama’ar da yawa  basu fahinci manufa da muhimmancin tausayi ba saboda rashin fahimta addini,shiyasa basu san yadda zasu tausaya wa al’umma ba tare da girmama su,kuma basu iya bambanta aiki maikyau da marar kyau, kuma basu tunani akan muhimmancin tausayi tare da duba menene Alkur’ani ya fada akan tausayi.,koda yaushe suna nuna halayen da zasu cutar da kansu da al’umma.;suna yin kuskure wajen magance wasu al’amura da suka taso ,saboda fahimtar su game da tausayi yan a cin karo da yadda Alkur’ani maigirma  ya bayyana tausayi da danganta  karsa da muhimmancin tausayi ga al’umma.Wani lokacin mutane sukan kai da komo wajen fahimtar tausayi, wanda daga karshe yakan zama kuskure tare da sabawa karantar war Alkur’ani maigirma.Irin wannan mummunar fahimta ga tausayi yakan zama cutarwa ga al’umma. Alummar da addini yasa ta rarraba zuwa kungiya  kungiya,za kaga shugabanni suna barin wasu mutane suna aikata wasu aiyuka batare da tunani da kuma  kallon riban  da zasu samu a ranar gobe (kiyama).Misali ,shugabanni  sukan kauda kai daga aikin  haramun da al’umma suke aikatawa,kuma ba tsawatar wa a lokacin ake aikata laifi da Allah (SWT) ya hana ko ya umurci al’umma dashi.     

A binda bayin Allah nagari suka zaba wa kansu a wannan al’amari, shine nuna wa juna tausayi da sauran jama’a, wanda zai jawo hadin kai da farinciki ga rayuwar al’umma duniya da lahira.Wasu lokuta kauna da tausayi da bayin Allah nagari ke nunawa al’umma yakan jawo masu matsala da zargi da wasu al’amura na  wahalar da kai. ,(an-nafs).Kuma suna shan wahala wajen fuskantar marasa gaskiya ta wajen nuna masu hanyar kwarai tare da jawo hankalinsu  su bar aikata haramun. Wannan shine gaskiyar tausaya wa juna, saboda kauce wa barna da illar sa,kuma  suna kokarin koyar da halin kwarai ta yadda za’a fahimci yadda Allah (SWT) ya koyar a cikin Alkur’ani maigirma,  wajen kare shi daga aikata aikin da zai kai shi ga shiga  wuta, kuma ba za’a bashi daman dawowa duniya ba ya gyara aikin sa.A bisa wannan dalili bayin Allah nagari suke karfafa mutane da su aikata aiki  nagari wanda zai sa su samu yardan Allah da tausayin sa, tare da samun Rahmar ubangiji shine shiga gidan Aljannah.Kamata mutum ya sani cewa aikata mugunta bazata kai mutum ga samun rahmar Allah (SWT) ba,kuma aika ta kuskure bisa  ganganci  yana jawo fushin  Allah (SWT) da azaba.

A bisa wannan dalili ,bayin Allah magari suke bin koyarwar Manzon tsira Muhammad (SAW) da halayen sa wanda Alkur’ani maigirma  ya bayyana mana.’’Kuma, lalle ,hakika kana a kan halayen kirki,manya". (Surat al-Qalam: 4)

A wata Ayar Allah (SWT)ya yabi manzon tsira (SAW) da halaye nagari: "Lalle ne,hakika ,Manzo daga cikinku yaje muku .Abin da kuka wahala da shi mai nauyi ne a kansa .Mai kwadayin ne saboda ku.Ga muminai Mai tausayi ne,Mai jin kai." (Surat at-Tawba: 128) A saboda wannan dalili bayin Allah (SWT) nagari da suka riki wannan umurni da  koyarwar Manzo (SAW)  suna masu nuna wa juna adalci da tausayi,tare da umartar al’umma su da aikata aiki  nagari saboda kwadaitar dasu samun tausayi da rahmar ubangijin su a gobe kiyama(lahira).

Allah yasa mu dace.
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support