Labari mai al'ajabi:-Mata kuyi hankali da mazajen ku!!!! ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 5 September 2017

Labari mai al'ajabi:-Mata kuyi hankali da mazajen ku!!!!

MATA KUYI HANKALI DA MAZAJEN KU.
*********
Wannan Labari na Rubuta Shine, Bisa Ga yardar Wacce abin ya faru da Ita, tare da Sharadin boye sunanta da kuma garin da take.

Ita wannan matar ta Gaya min Cewa, Yanzu haka suna kotu ta kai mijinta da Iyayenta kara, da farko dai ta dawo gidansu tabukaci iyayenta da su raba aurenta da mijinta. Saboda zai lalata mata rayuwa a banza.

Da farko Iyayen Sun tambayeta dalilin da yasa take son a raba auren amma taki gaya musu, maimakon ta gaya musu gaskiya sai ta ki gaya musu gaskiya tace, "Ita dai Allah ne ya cire mata son shi."

Iyayenta Suka ce, Hoho su bazasu raba auren ba, Na farko dai Alhajin yana mutun ta su, tare da biya musu duk wasu bukatu da suke so, to su taya zasu ce ya sake ta? Suka nuna mata su ba zasu iya wannan abin kunyar ba.

Lokacin da taga Iyayenta sunki amincewa da bukatarta sai ta je kotu ta bukaci a raba aurenta da mijinta. Alkali ya tambaye ta dalili amma sam taki ta gaya masa dalilin faruwar haka.

Sai ta bukaci koda Hul'I ne ita ta yarda ayi domin Ita bazata koma gunsa ba, da ta koma gunsa gwanda ta zama karuwa, haka ta gaya wa Alkali. Jin wannan furucin na ta Sai Alkali ya nemi Mijin yayi hakuri ya sallame ta mana Yaje ya auri ya sake aure.

Amma sam mijin yace Shi ba zai sake ta ba, A gefen Mahaifiyarta kuma tayi Rantsuwa Cewa, Muddin wannan matar ta rabu da wannan alhajin to bata yafe mata ba duniya da lahira.

Mahaifinta ne kawai ke tausaya mata, Shima kuwa ba sosai ba domin har dukanta yayi a kwanan baya lokacin da mijin ya zo ta rika zaginsa tana ci masa mutunci.

Innalillahi Wa Inna Ilaihin Raji'un, lokacin da ta gaya min abinda ke faruwa sai da hankalina ya bar jikina domin kuwa na dau ki mintukka ba ce da ita komai ba sai daga baya.

Shi Wannan mijin nata ya kasance kafin ya sadu da ita ta gaba sau daya yana saduwa ta baya (Anal Sex) da ita sau goma (wa'iyazubillahi).

Lokacin da na tambayeta keko me ya kaiki yarda da shi? Sai tace, Alkawali yayi ba zai mata Kishiya ba, kuma zai kaita makka sannan zai bata Kuddi ta rika juyawa." Ta kara da cemin, Sannan ya gaya mata wannan hanya ita ce ke kawo masa kuddi muddin ya baryin haka to zai daina samun kuddi. (Innalillahi KAIDAI KAGA MUTUM).

Tace Lokacin da aka fara babu wata matsala da ta fuskanta sai dai daga baya sai ta rika jin tana wani wari wanda Ita kanta bata san daga Ina yake fitowa ba, haka Kuma Idan tana jin kashi idan bata je taji ba yanzu yanzu zai zubo mata, sannan duk lokacin da ta tashi daga bacci takanga wasu kananan tsutsotsi a jikin bantan ta (wa'iyazubillahi). Yanzu abinda ke damunta Shine:

Mahaifiyarta ta tsine mata akan kada ta kuskura ta rabu dashi.
Sannan tana gudun kada ta fayyace wannan mummunan abu da ya faru da ita mutane su guje ta har daga karshe ta rasa wanda zai aure ta.

Wannan Baiwar Allah tayi Nadamar wannan abu da ya same ta sannan ta bukaci a taimake ta da Addu'ar Allah ya yaye mata wannan musiba, Sannan ta Bukaci da In sanarwa Jama'a musamman ma mata domin su kula sosai da Sosai.

Ni kuma Na sanar muku Ina Kyautata Zaton duk wanda Ya samu wannan Sako to ya turawa 'yan Uwa Domin Ba'a fara ba ya fi a fara.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Wed 30-08-2017
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support