Illolin gulma 02 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 30 September 2017

Illolin gulma 02

```★★★ILLOLIN GULMA★★★```
~~~~~~~~~~2~~~~~~~~~~
*Zauren SA'ADATUL-MUSLIM*
.
_Wannan shine bayani na biyu kuma muna magana akan Gulma_
.
_Gulma fa jama'a ina kara jaddada mana cewa wallahi gulma yanda ta yawaita acikin wannan Al'ummar babu maza ballan tana mata, kai babu manya ballan tana kanana, abin yakai ya kawo hatta acikin masallatayyar mu an mayar dasu wajaje na gulma, abin dai ya zama kamar wani Ibadah duk inda zakaji ance ga wani majalisi, to wallahi zaka samu ba majalisi bane wajen gulma ne, matsalar ba anan kadai ba hatta acikin makarantu na Islamiyya an mayar dasu sun zamo wajajen gulma, kai 'yan uwa abin fa kamar gāsa akeyi hatta a social media Facebook whats app da sauran wajajen fira akan samu zaure wanda kawai aikin su shine  gulma! mun samu wani lokaci da wuya kasamu mutum biyu zuwa uku sun zauna suna fira har su tashi basuyi gulman dan uwa musulmi ba, 'yan uwa abinfa yayi kāmāri da yawa sai dai mu nemi tsarin Allah daga wannan musifa ta Gulma_
.
_Cin naman 'yar uwarki shine ki ambaci wani al'amari nata wanda idan dai har tana nan kika ambaci wannan kalmar zataji haushi, wannan shine ma'anar gulma wato ma'nar gulma itace kaine zaka fadi wata magana akan dan uwanka idan har yana wajen kayi wannan maganar tofa zaiji haushi, wato idan kayi magana a bayan idon dan uwan ka wato bazai lamunce ba bazai yarda ba, gashi halin nata ne kika ambata amma dai idan har tana wajen ranta bazaiji dadi ba wannan fa shine ma'ana gulma,  'yan uwa saboda Illar Gulma Allah madaukaki bai barwa Annabi Saw ragamar haramta Gulma ba, shima da kansa sai da ya haramta mana yin gulma, Lā haula walā Quwwata Illā Billāh  'yan uwa mune fa muke karanta Alqur'ani mu mune Al'ummar Annabi Muhammad saw kuma ayar da Allah ya haramta gulmar 'yan uwa dani dake da ku masu karatu wallahi muna karanta wannan ayar, amma gaba daya bamuyin aiki da ita,_
.
_Gashi kuma sanin kanmu ne cewa dukkan inda muka samu umarni acikin alqur'ani to yin aiki da wannan umarnin wajibi ne, haka kuma dukkan inda muka samu wani hani acikin Alqurani tofah wannan hanin dole ne mu hanu matukar muna son mu samu rabo a ranar qiyamah, zamu dauki aya guda daya acikin Alqur'ani da Allah ya haramta gulma, daga nan sai mu dauki wasu takaitattun hadīsai da sukayi magana akan gulma,! Allah ta'ala ya shiryar damu,_
.
 _Zamu dakata anan sai mun hadu a darasi na gaba_
.
*Hussaini Ibnu Taimiyyah Kuriga*
.
→ A yanzu haka zaku iya bibiyar zauren SA'ADATUL MUSLIM ta shafin sada zumunta dake Facebook ta cikin wannan link din
https://free.facebook.com/Saadatul-Muslim-Islamic-Group-Chat-1017855871594468/?ref=opera_speed_dial_freefb
.
→ Ga masu sha'awar shiga zauren SA'ADATUL MUSLIM sai su aiko da cikakken Suna da adreshi izuwa ga numbar mu +2348052975857 ta whatsapp ‬


Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support